Tuesday, 21 November 2017

Mace-Guda-Daya-Tilo-Part-1-One

                                        Matashin saurayine sanye da kayan yan
                                    bautar kasa (N. Y. S. C) kayan sunyi mutukar
                                   yimasa kyau, tsaye yake agaban allo yana yiwa
                                   dalibai yan department of sociology lecture din
                                     biology, a jami'ar tarayya dake jihar bauchi,

                                    kowanne dalibi ya nutsu yana sauraron lecture
                                   din domin babu karya malamin akwai iya darasi 
                                    kuma akwai zakin murya radau,wannan shine
shigarsa hall din na 3 ,yauma kamar kullum ya
kwashe fiyeda awa 1 yana yimusu lecture akan
introduction to biology, kwas kwas sukaji tafiyar
takalmi alamun ana shigowa cikin hall din,
hankalin kowa yakoma kanta, jiyowa shima yayi
yabita da kallo daga sama har kasa, farace
sosai dan har yellow take dan tsabar fari, bata
da tsayi sosai amma tana da dan jiki,
idanuwanta manya ne farare tas,tanada dogon
hanci da dan mitsitsin baki, tana sanye da wani
pink din leshi da mayafinsa takalmin kafarta
kuwa mai dan karen tsinine shima pink
hannunta rike da jaka pink colour, kanta tsaye
ta nufi inda zata zauna, he! Taji malamin ya
fada ko jiyowa batayi ba taci gaba da tafiyarta.
[3/11, 6:16 PM] Ummi A'isha: MACE GUDA
DAYA TILO...2⃣


Na
UMMI A'ISHA
Cike da haushi yabi bayanta yasha gabanta
tare da nuna mata hanyar fita get out from my
class taji yafada, idanuwanta ta bude sosai
tafara kallonsa farine tas dogo mai tsananin
kyau yana da idanuwa sosai hancinsa tamkar
biro kuma yana da yar kiba daidai misali ita
kanta tasan yanada kyau kuma ya hadu kallon
banza ta wurga masa tare da Jan wani dogon
tsaki, mamaki ne ya kamashi dan babu macen
da ta taba yi masa tsaki sai wannan yarinyar
yar rainin hankali, tsawa ya daka mata yace
who are you dazaki shigo min class yanzu? Me
kike takama dashi? Ke yar gidan uban waye?
Gaba daya ajin yayi tsit kowa ya zuba ido yana
kallonsu domin idan da sabo to sun gama
sabawa da halin wannan dalibar wani mugun
kallo ya bita dashi sannam yace oya carry your
legs and get out from my class tun kafin na
wulakanta ki, ni banma taba ganin wannan
fuskar taki acikin class dina ba, ita kuwa gaba
daya bakin cikin duniya yagama rufeta batare da
tace masa ko kala ba tajuya tafice daga cikin
hall din zuciyarta cike da bacin rai, lalle gayen
nan yau xan nuna masa ko ni wacece zaisan
dani da sauran matan da yasaba yiwa wulakanci
akwai banbanci ayau sai naga waye ubansa a
kasar nan.
[3/11, 6:18 PM] Ummi A'isha🏻: MACE GUDA

DAYA TILOģ

Na
UMMI A'ISHA
Dawowa yayi yahau kan step din yaci gaba
da lecture din daya keyi, Director din makarantar
ne yashigo cikin hall din shida mukarrabansa
nan da nan idon kowa ya koma kansu wanda
ciki harda shi kansa malamin, dasauri director
din yazo gabansa yana cewa me yahadaka da
wannan yarinyar junaida mukhtar? Kasan ko
wacece ita? Bude baki copper din yayi tareda
niyyar yin magana amma cikin tsawa director
din ya katse shi tare da cewa look Lamin kaifa
ba staff dinmu bane service kawai kazo yi dan
haka mun dakatar dakai daga wannan
aikin,yanzu ka biyoni office inada magana dakai
yana kaiwa nan ya juya yafita shida wadanda
suka rakoshi, ajin kuwa tsit kakeji kamar ruwa
yacisu shi kuwa malamin wanda aka kira da
lamin kayansa yashiga tattarawa ya rufe laptop
dinsa ya saka acikin jakarta ya yiwa daliban
sallama wadanda akalla zasu kai kimanin dari
biyu kasancewar combined lecture ne
[3/11, 6:22 PM] Ummi A'isha: MACE GUDA
DAYA TILO
ģ

Na
UMMI A'ISHA
Gaba daya yan ajin jikinsu yayi sanyi domin
wannan bashine karo na farko da dalibar tayi
sanadiyyar korar malaman makarantar ba,
ahankali ya gama hada kayansa cikin jakar ya
dauka ya rataya akafadarsa ya sauko ya futa
daga cikin hall din, yana fita hall din ya cika da
surutun daliban dake ciki, wasu tausaya masa
suke wasu kuma bakin cikin tafiyarsa suke
yayinda wasu kuma suke Allah wadai da halin
wannan dalibar mai suna junaida mukhtar.
Kansa tsaye ya nufi admin block,office din
director ya shiga suna zaune shida students
affairs da registerer da hed of department can
gefe kuma wannan kyakkyawar yarinyar ce
zaune tana kallonsa, da sallama yashiga suka
amsa tareda nuna masa kujerar da zai zauna,
yana zama director yafara balbale shi da fada
tareda cewa yazama dole kabata hakuri kuma
ka nemi afuwarta akan abinda yafaru dazu baki
ya bude cike da mamaki wai shine zai bawa
wannan yarinyar hakuri instead ace itace zata
nemi afuwarshi kallo yabisu dashi daya bayan
daya sannan yace impossible yaza ayi ace nine
zan bata hakuri bayan itace tayi min laifi? Head
of department ne ya katse shi ta hanyar cewa
kasan yar gidan waye kuwa? Ko yar gidan waye
wlhi bazan bata hakuri ba kallonsa suka farayi
cike da mamaki director yace to ai kuwa tunda
bazaka bata hakuri ba yazama dole kabar
makarantar nan ayau.
[3/11, 6:23 PM] Ummi A'isha: MACE GUDA
DAYA TILO
ģ

Na
UMMI A'ISHA
Mamakine karara ya bayyana akan fuskarsa
domin kuwa babu dalilin da zaisa akoreshi akan
kawai ya hukunta dalibarsa wacce ta karya
dokarsa, wata xungureriyar takarda director ya
miko masa yace gashi ka zaba acikin biyu
nafarko ko kabawa junaida hakuri ko kuma ayau
dinnan ka bar mana makarantar nan domin
bazamu zuba maka ido ka yimana sanadin
aikinmu ba, wannan yarinyar babanta shine
permanent secretary na education kuma shine
Head of service na wannan state din dan haka
kazabi daya, shiru lamin yayi yana tunani wato
dan babanta ne head of service shikenan sai ta
raina mutane? Shi ai ya zata duk wannan
kafafar da take babanta ne governor dama head
of service ne kawai? Wani guntun tsaki yaja
aransa yace lallai nima dan bakusan waye ni ba
shiyasa kuke neman wulakanta ni,ni ai ubana
yafi nata matsayi tunda secretary to the state
government ne kaf state dinmu ubana shine na
3 daga governor sai deputy sai ubana amma
ban taba nunawa ba registerer ne ya katse masa
tunani ta hanyar cewa lamin kaifa muke jira kayi
magana kallonsu yayi sannan ya juya ya kalli
yarinyar yace wlhi bata isa nabata hakuri ba
nazabi barin makarantar, takardar ya karba ya
tashi yafita daga cikin office din ya nufi motarsa
wadda ke ajiye awurin da aka tanada domin
ajiye motoci.
[3/22, 7:56 PM] Ummi A'isha🏻: [3/15, 7:05 AM]
Ummi A'isha🏻: MACE GUDA DAYA TILO
ģ

Na
UMMI A'ISHA
Motarsa kirar Toyota corolla yabude ya shiga
ya fita daga cikin makarantar ,gudu yake
shararawa sosai kamar wadda zai tashi sama
yafita daga garin bauchi ya nufi birnin yola.
Karfe 3 dai dai yashiga cikin yola Chief olusegun
obasanjo housing estate ya nufa, ahankali yake
tukin har ya iso tangamemen gidan nasu wanda
yake cikin jerin gwanon gidajen, hon yayi mai
gadi ya bude masa gate din yashiga cikin gidan
securities sai daga masa hannu suke yi ajiye
motar yayi a muhallinsa sannan ya tasamma
cikin gidan, babban falon gidan ya shiga daya
daga cikin kannenshi ya hango kwance cikin
luntsumemiyar kujera tana kallon Indian film
sallama yayi dasauri ta dago tana cewa oyoyo
yaya lamin karasowa ciki yayi yana cewa
wacece? Hasna ce ko husna? Murmushi itama
tayi tace yaya kenan wai kai meyasa baka
ganemu? Dariya yayi mata sannan yace to
mummy da daddy ma basa ganeku balle ni da
bani na haifeku ba dariyar itama tayi sannan
tace to husna ce hasna na kitchen tana yimana
fried indomie murmushi yayi yace sarakan
kwadayi kenan ina mummy? Mummy tana side
din dad tabashi amsa mikewa yayi ya nufi side
dinshi.
[3/15, 7:08 AM] Ummi A'isha🏻: MACE GUDA

DAYA TILOģ

Na UMMI A'ISHA
Dakinsa yashiga ya zauna ya zubawa carpet
din dake malale acikin dakin ido, tunanin
matakin da zai dauka akan wannan yarinyar shin
me take takama dashi? Yanzu kenan duk burin
da ya dauka ya rushe? Babban burinsa shine
yayi lecturing lokacin service dinsa domin yana
kaunar koyarwa a jami'a amma yau gashi wata
MACE GUDA DAYA TILo tayi masa sanadi ta
rusa masa duk budget dinsa ai kuwa yazama
tilas ya rama wannan wulakancin da tayi masa
da wannan shawara ya tashi ya shiga hadadden
toilet dinsa yayi wanka ya fito yashirya cikin
wata green din t shirt mai hoton heart ajiki sai
blue din jeans ya taje sumar kansa ya fesa
turaren smart collection ya fito, falon
mummynsa ya wuce yana shiga ya tarar da ita
zaune cikin kawatacciyar shiga tana waya
gefenta yan biyunta ne zqune suna cin
indomie,kusa dasu yaje yazauna yana fadin
hasna kin gama girkin dasauri kanwar tasa ta
kalleshi tana fadin lah yaya lamin yaushe ka
dawo? Ban jima da dawowa ba ya bata amsa
dai dai lokacin mummyn tasu ta gama wayar ta
kalleshi tana cewa babana saukar yaushe? Wlh
dazu nadawo mummy daddy yana gari kuwa?
Kallonsa tayi tace bakuyi waya bane? Dazun nan
yadawo daga Holland kaje ka sameshi yana falo
mikewa yayi ya nufi falon mahaifin nasa.
[3/15, 7:12 AM] Ummi A'isha🏻: MACE GUDA

DAYA TILOģ

Na UMMI A'ISHA
Ahankali yake ratsa falikan har ya isa na
mahaifin nasa ya sameshi zaune yana hutawa
sallama yayi masa sannan ya nemi wuri ya
zauna yafara gaida shi cikin murmushi mahaifin
nasa ya amsa sannan yace lamin har kadawo
daga bauchin? Jikinsa asanyaye yace dady sun
sallameni sunce sai dai naje wani wurin nayi
service din kallonsa mahaifin nasa yayi sannan
yace laifin me kayi musu? Kansa ya sunkuyar
kasa sannan yace babu laifin komai daddy to
yanzu ya zakayi? Ya tambayeshi dama daddy
cewa nayi yanzu zan koma can N. Y. S. C
Secretariat din na sanar musu inyaso sai ayi
posting dina Bayero university kano ina ganin
hakan zaifi, to shikenan Allah yasa hakan shi
yafi alkhairi mahaifin nasa yace dashi amin ya
amsa sannan yatashi ya fita daga cikin falon.
Ita kuwa junaida tana tashi daga office din
director tashiga sabuwar motarta kia 1 door ta
nufi gidansu dake unguwar area 7 tana isa ta
wuce dakinta ta jefar da jakarta, mayafinta,
takalminta, wayarta ta haye gadonta ta kwanta
rufe idonta keda wuya tafara ganin wannan
saurayin matashin yana yimata gizo gaskiya
babu karya ya hadu zuciyarta taji tafara dukan
uku uku kamar zata tsage, idanuwanta ta bude
sannan ta mayar ta rufe still shi din dai take
gani lokacin da yake yayyafa mata masifa acikin
hall din.
[3/15, 7:13 AM] Ummi A'isha🏻: MACE GUDA

DAYA TILOģ

Na UMMI A'ISHA
Zaune ta tashi cikin sauri, Fara zagaya cikin
dakin nata tayi sannan ta saki wani kayataccen
murmushi toilet ta shiga ta silla wanka sannan
ta fito ta sanya wata doguwar riga ta shan iska
ta nufi falo acan ta hango mahaifiyarta zaune
tana kallo karasawa tayi cike da shagwaba ta
fada kan cinyarta tana cewa umma nifa yunwa
nake ji dasauri takalleta tace haba autana me
yasa kike son zama da yunwa kira tafara
kwallawa daya daga cikin yan aikin gidan
dagudu ta runtumo tazo ta durkusa agabansu
kallon junada ta yi tace auta me zaki ci?? A
yangance tace ta dafa min indomie with egg da
sauri mai aikin ta tashi ta nufi kitchen domin
aiwatar da abinda aka sata ita kuma taci gaba
da zubawa uwar shagwaba.
[3/15, 7:15 AM] Ummi A'isha: MACE GUDA
DAYA TILO..
ƒ£0⃣

Na UMMI A'ISHA
Tun da sassafe lamin ya baro garin Adamawa
ya nufi bauchi gudu yake babu kakkautawa ya
kure A. C din motar ya kunna wakar no one be
like you yana saurare amma acan kasan ransa
kuwa abinda zai aiwatar kawai yake tunani.
Karfe takwas ya shiga cikin bauchi dan haka
wani guest house ya zarce inda zai huta. Sai 10
ya fito yashiga cikin garin kofar jami'ar yaje ya
yi packing yana ganin shige da ficen daliban
yana nan xaune acikin motarsa ya rurrufe glass
din wanda ya kasance mai mutukar duhu ne na
waje baya ganin na ciki sai na cikine ke hango
na waje, wata mota pink colour ya hango tana
tahowa kirar new discussion R888 sai datazo
saitinsa sannan yaga ashe wannan yarinyarce
junada aciki tasha ado tamkar wata sarauniya
komai blue nan da nan ta kutsa kan motar tata
cikin makarantar shi kuwa murmushin mugunta
yayi tareda fadin yarinya kin tabo gidan rina dan
haka zaki yi bayani.
[3/22, 7:56 PM] Ummi A'isha🏻: [3/17, 9:52 AM]
Ummi A'isha🏻: MACE GUDA DAYA TILO..
ƒ£1⃣

Na
UMMI A'ISHA
Yana nan zaune har ya hango adam dama
shi yake jira, Adam daya daga cikin dalibansa ne
wanda yafara koya musu kuma course mate din
junada mukhtar ne shigowa motar adam din
yayi sannan yafara gaida lamin ta hanyar cewa
morning sir, morning lamin din ya amsa yace
dama zuwa nayi kabani duk labarin da kasani
akan wannan yarinyar junada mukhtar murmushi
Adam yayi sannan yafara bashi labarin. Alhaji
mukhtar Magashi shine mahaifinta kuma
asalinsu yan garin bauchi ne cikin karamar
hukumar Giyade babanta ya rike madafan iko da
yawa daga karshe aka bashi mikamin head of
service na wannan jahar matarsa 1 da yaransu
uku junada ce yar auta sai yayunta maza guda 2
Khalid da Amir, yar gatace ta karshe kasancewar
ita kadai ce mace kuma gata yar auta komai
daka sani na rayuwa yimata ake bata da wata
matsala sai kwaya daya.
[3/17, 9:54 AM] Ummi A'isha🏻: MACE GUDA

DAYA TILO...ƒ£2⃣

Na
UMMI A'ISHA
Matsalarta shine bata son karatu ko kadan
gata shagwababbiya ce ta karshe amma duk da
haka mahaifinta yana hukuntata idan ta aikata
ba dai dai ba sai dai ita mahaifiyarta tafi batata
don bata tsawatar mata idan tayi ba dai ba,
tunda muka shigo makarantar nan bata zuwa
lecture sai time din data gadama, bata
respecting din malamai balle yan uwanta dalibai
bata da lokacin tsayawa tayi karatu amma kuma
babu malamin da ya isa yabata carry over
saboda director yana daure mata gindi, yana iya
korar mutum akanta saboda kawai yana jin
tsoron kar ta fadawa mahaifinta abashi query
bayan kuma shi mahaifinta ba irin wadannan
mutanen bane masu zarmewa akan yayansu, ka
ganta nan har muka shiga level 300 bata taba
samun carry over ba alhalin kuma ba karatun
takeyi ba. Wani matashin murmushi lamin yayi
tabbas yanzu ya samu hanyar da zai rama
abunda tayi masa ta hanya mai sauki juyawa
yayi ga Adam yayi masa godiya sannan ya yi
masa sallama yatashi motarsa ya bar wurin,
garin kano ya nufa yana tafe yana nishadi ya
kunna wakar you are my African queen ahaka
har ya isa B. U. K.
[3/17, 9:56 AM] Ummi A'isha🏻: MACE GUDA

DAYA TILO..ƒ£3⃣

Na
UMMI A'ISHA
Yana isa ya kai takardunsa cikin sa'a sukayi
accepting dinsa musamman ma da suka ga
cewar ba a Nigeria yayi karatunsa ba a Malaysia
yake yi, psychology department suka turashi
suka bashi yan level 100 inda zai daukesu
Biology, sati 1 suka bashi tareda bashi inda zai
zauna amma bai karbi masaukin ba kasancewar
yanada inda zai zauna. Karfe 4 yagama abinda
zaiyi yabar cikin makarantar ya nufi yola. Bai
isa garin yola ba sai kimanin karfe 7 nadare
yana zuwa mahaifinsa ma na karasowa dan
haka cikin gidan ya shiga yajira karasowar
mahaifin nashi wanda bodyguard dinsa suka
ysnyameshi kamar wanda za adauke,da
fara'arsa ya tari dan nasa yana fadin tafiya tayi
sauri my son dafatan andace? Murmushi yayi
sannan yace yes dad sunyi accepting dina dafa
kafadarsa uban yayi tareda jan hannunsa suka
jera suna tafiya tamkar wasu abokai har suka
karasa cikin falon uban sannan shi lamin din ya
juya ya wuce side din mummy yana shiga ya
tarar da babban yayansa yana zaune yana cin
abinci akan dinning wajensa yakarasa yabashi
hannu suka gaisa sannan shima ya nemi wuri ya
zauna yace broz nabar bauchi university fa na
koma kano murmushi yayan nasa yayi wanda
suke mutukar kama amma shi bakine sabanin
lamin wanda yake fari sol, dubansa yayi yace to
nidai ina baka shawara wlhi babu kai babu yan
matan jami'a, dan nasan halinka da shegen
neman mata.
[3/17, 9:59 AM] Ummi A'isha🏻: MACE GUDA

DAYA TILO...ƒ£4⃣

Na
UMMI A'ISHA
Kai ko tsoron Allah bakaji balle tsoron
wadannan cutukan na zamani, rai lamin yabata
sannan yace kaifa kanada takurawa wlh
shigowar mahaifiyarsu ne yasashi yin shiru
domin baya son taji zancen da yakeyi
kasancewar yanada yakinin duk gidan babu
wanda yasan yana neman mata in banda yayan
nasa cikeda murna tace sannu babana shima
cikin sigar shagwaba yace yawwa mummy dama
nazo miki da wani albishir murmushi tayi tace to
Allah yasa alkhairi ne ai kuwa mummy alkhairi
ne kuma nasan zakiyi farin ciki sosai kallonsa
suka tsaya yi itada yayan nasa tace to fadi inji
cikin farin ciki yace na samo matar aure a
bauchi dan haka kisanar da dad aje a tambayo
min domin aure nake so, wani farin cikine ya
lullube uwar tace to Allah yasa albarka kuma
naji dadi bayan kagama karatu za ayi bikin?
Dasauri yace no nanda 3 months nake so ayi
cikin mamaki tace to zai yiwu ahada da na
abdulrahman yayankane? Yes mum haka nake
so ayi cikin fara'a tace to Allah ya yarda tatashi
ta fita daga cikin falon. Yayansa ne ya kalleshi
yace ai gara kayi auren yafi maka amma kana
yaronka dakai sai jarabar mata just 26 years?
Koni da nake 29 bana bin mata sai kai? Cikin
kunkuni lamin ya mike yabar cikin falon ya nufi
side dinshi aransa kuwa fadi yake wannan
dinma da zanyi ai na ramuwar gayya zanyi bana
Allah bane.
[3/17, 10:00 AM] Ummi A'isha🏻: MACE GUDA

DAYA TILO...ƒ£5⃣

Na UMMI A'ISHA
Yana shiga hadaden dakinsa wanda ya
kawatu mutuka da kayan alatun more rayuwa ya
fada saman gado ya jawo wayarsa BlackBerry
B210 Vicky yakira daya daga cikin yanmatansa
ringing 2 ta dauka cikin harshen turanci tafara
gaida shi murmushi yayi yace nayi missing dinki
daga can kamar zatayi kuka tace nafika damuwa
da rashinka kusa dani yanzu yaushe zakazo?
Silin din dakin ya kurawa ido yace gaskiya Vicky
zaki dade baki ganni ba amma next week zan
shigo kano to idan nazo i will call you murmushi
tayi tace ok sai najika i luv you, luv you too ya
amsa mata ya ajiye wayar ko minti 2 ba ayiba
wayar tasa tasoma ruri hannu ya mika ya dauko
yana dubawa yaga Jenifer ce cikin murmushi
yaje hello madam j how are you? Daga can ta
amsa da fine my Prince.
[3/22, 7:56 PM] Ummi A'isha🏻: [3/22, 4:21 PM]
Ummi A'isha🏻: MACE GUDA DAYA TILO..
ƒ£6⃣

Na
UMMI A'ISHA
Kamar zata saka kuka tace yaushe zamu
hadu? Wani malalacin murmushi yayi sannan
yace very soon but yanzu ina yola ne kin san
babu halin kizo amma idan nasamu time zanzo
dakaina cike da jin dadi tace to ina jiranka i love
you me too yabata amsa ya kife wayar. Daya
wayar tashi ce ta soma kara ya dauka ya duba
sunan Mary yaga ajikin screen din cikin sauri ya
daga yace hello my Mary yakike? Daga can tace
abnormal murmushi ya aika mata dashi yace
what's wrong? Cikin shesshekar kuka tace
kamanta dani kwana biyu baka nemana
rarrashinta yafara yi domin duk cikin yanmatan
sa itace star yafi ji da ita domin Mary akwai
kyau ga diri shiyasa ma yafi sonta fiyeda sauran
dakyar ya samu ya lallasheta tadaina kukan
sannan yayi mata alqawarin zai tura mata kudi
ta account dinta sai ta yanki ticket din jirgi daga
Lagos tazo kano ta sameshi saida yayi da gaske
sannan ta hakura sukayi sallama yana ajiye
wayar yaga yayansa daga bakin kofa yana tsaye
yana kallonsa fuskarsa babu walwala yace lamin
abinda kakeyi baka kyautawa wai kai me yayan
arnan nan suke baka ne ka manne musu? Wlh
kaji tsoron Allah dan babu mamaki yanzu yana
fushi dakai kuma inajin ma har giya kana sha
sai asannan lamin yayi magana yace ni babu
abinda nake sha nasan dai ina neman mata
amma bana shan ko sigari balle giya.
[3/22, 4:22 PM] Ummi A'isha🏻: MACE GUDA

DAYA TILO...ƒ£7⃣

Na
UMMI A'ISHA
Harara ya wurga masa sannan yace kalli lips
dinka yadda sukayi ja ahaka xakace min baka
shan giya na yarda? Kallonsa yayi yace yaya sai
dai idan sharri zaka yimin amma wlh bana shan
giya hararsa ya kuma yi yace kaji dashi dai ya
juya yayi ficewarsa shi kuwa lamin tashi yayi ya
shiga toilet domin watsa ruwa. Abangaren
junada kuwa tun ranar data sa aka kori lamin
duniya tayi mata zafi domin ta tsinci kanta
dumu dumu cikin kaunarsa gashi bata san a
inda yake ba bare tasa anemo mata shi, yauma
ranta abace ta shirya cikin wani brown din
material ta nufi sch amma sam zuciyarta babu
dadi gaba daya ranta abace yake kuma ko yaya
ta rufe idanuwanta shi take gani abinda yafi
tsaya mata arai shine yadda kullum sai tayi
mafarkin kyakkyawar fuskarshi, ranta ajagule ta
fito daga dakinta ko ummarta bata yiwa sallama
ba ta fita sabuwar motarta Prado baka ta dauka
ta nufi makarantar zuciyarta cike da fatan dama
taga wannan matashin saurayin.
[3/22, 4:24 PM] Ummi A'isha: MACE GUDA
DAYA TILO...
ƒ£8⃣

Na
UMMI A'ISHA
Da wannan tunanin ta isa cikin makaranta kowa
mamakin canjawarta yake tun ranar da abin
yafaru bata kara yiwa kowa maganar bacin rai
ba sannan yanzu ta daina makara da wuri take
zuwa school sabanin da dasai lokacin data
gadama kuma babu wanda ya isa ya hanata
shiga lecture, ahankali tashiga hall din ta zauna
ziciyarta cike da dana sanin fadawa director
datayi har aka kori wannan dan bautar kasar da
haka tagama sauraron lectures din ta tashi ta
tafi gida. Shi kuwa lamin tuni yafara zuwa
lecturing a kano B. U. K wani dan madaidaicin
gida ya kama a unguwar jan bulo kabuga tuni
budurwarsa Vicky ta yi masauki agidan tana
tafiya Mary tazo, haka ya rinka sheke ayarsa
batare da iyayensa sun sani ba dama ko lokacin
da yake Malaysia haka haka yake ajiyesu
agidansa daga wannan ta tafi wannan zatazo.
Yan matan jami'a kuwa ba acewa komai domin
ganinshi kyakkyawa mai class kuma ga kudi nan
da nan suka Fara cusa kansu wurinsa sai dai
har yanzu babu wadda ta samu shiga domin shi
baya harka da hausawa duk yan matansa
Christian ne babu musulma ko daya kuma
bashida standard budurwa domin bai shirya aure
yanzu ba sai auren ramuwar gayya.
[3/22, 4:25 PM] Ummi A'isha🏻: MACE GUDA

DAYA TILO...ƒ£9⃣

Na
UMMI A'ISHA
Yau tunda yagama lecture yakoma gida yafara
hada kayansa ya gama Mary dake kwance tana
bacci yafara tashi dakyar ta tashi tana faman
murtsuke ido tana tambayarsa har yadawo eh
ya amsa mata sannan yace kitashi ki shirya
kitafi sai next week zan dawo kinga yanzu ni
nagama shiryawa kamar mai shirin yin kuka tace
to sai munyi waya tashi yayi yadau jakarsa
yatafi tareda bar mata sallahun idan tagama ta
rufe gidan. Karfe 2 na rana ya isa gida mummy
yatarar zaune afalo yan biyunta sun zagayeta
sai surutu suke mata ganinsa da sukayi yasa
suka dan nutsu suna fadin oyoyo yaya harara
yabisu da ita yace kunzo kun wani zagayeta
kamar wasu kananan yara, ke hasna kin share
min dakin dana saki? Dasauri tace yaya bani
bace sai dai ko husna cikin sauri itama tace wlh
bani bace banza yayi dasu domin dama haka
suke masa irin wannan rainin hankalin idan yasa
daya aiki to idan batayi ba sun rika cewa wance
ce itama dayar tace ba ita bace ,mummy ya
kalla yace mummy ina wuni cikin fara'a tace lfy
babana kallonta ya sakeyi yace yakukayi da
dady akan maganar nan? Dariya tayi tace kaifa
kafiya zumudi ai mun gama maganar dashi
ashema yar gidan Alh mukhtar magashi ce? Ai
tuni dadynku yayi masa magana kuma yace bai
mata miji ba dan haka yabaka ita yanzu saura
aje ayanke rana, farin ciki ne ya cikashi ya mike
ya nufi side dinshi.
[3/22, 4:27 PM] Ummi A'isha🏻: MACE GUDA

DAYA TILO..ƒ£0⃣

Na
UMMI A'ISHA
Zuciyarsa fes ya shiga dakinsa yasamu wuri
ya zauna yana tunanin ta inda zai bullowa
wannan yarinyar junada. Mukhtar wani
malalacin murmushi yayi dalilin samo abinda
zaiyi mata cikin haka yaji phone dinshi tana kara
ahankali ya cirota daga cikin wandon jeans din
dake jikinsa Angelina yagani a rubuce tsaki yayi
ya ajiye wayar batare da ya daga ba daga
karshema da yaga tana neman damunshi sai ya
kashe wayar gaba daya. Ita kuwa junada kullum
da tunanin lamin take kwana take tashi kafin ta
ankara sonsa yagama cika zuciyarta, yau kamar
kullum ta dawo daga school ta kwanta tayi
bacci ta huta sannan tayi wanka ta fita zuwa
falo amma bataga mahaifiyarta ba dan haka ta
wuce dakinta adakin ta sameta tana zaune
bakin gado tana waya kusada ita taje ta zauna
tana sauraronta har tagama, gamawarta keda
wuya ta juyo gareta tana cewa junada har kin
tashi daga barcin? Dazu nashiga dakin naki
naga kina bacci dama mahaifinki ne yabani sako
nasanar dake yabada ke ga dan abokinsa ras
junada taji gabanta yafadi kallon mahaifiyar tata
tayi sannan tace a ina yake? Murmushi uwar
tayi sannan tace dan gidan Alh kabir sulaiman
yola ne mahaifinshi shine SSG na Adamawa
state kuma yanada sarauta makaman Adamawa
Turakin yola gashi kuma classmate din
mahaifinki ne domin tare sukayi makaranta
kedai kawai abinda nake so dake shine kiyi
kokari kiyi biyayya insha Allahu zakiji dadi agaba
don kin san mahaifinki bazai taba zaba miki
mijin da ba nagari ba ita dai junada shiru tayi
batace komai ba domin hankalinta yagama tashi
amma duk da haka ta kuduri niyyar yiwa
mahaifinta biyayya ahankali tace to umma naji
abinda kikace Allah ya zaba min mafi alkhairi
cikin jin dadi mahaiyarta tace amin Allah yayi
miki albarka.
[3/22, 7:56 PM] Ummi A'isha: [3/22, 4:37 PM]
Ummi A'isha🏻: MACE GUDA DAYA TILO...
ƒ£1⃣

Na
UMMI A'ISHA
Tuni mahaifin lamin ya shirya shida yan
tawagarsa yaje gidan su junada domin nemawa
dansa aurenta batareda wani bata lokaciba
mahaifinta ya amince tareda sanya ranar auren
dai dai da ranar da za ayi na yayansa
Abdulrahman sun rabu cike da farin ciki da
girmama juna, ita dai junada bata cewa domin
dama bata damu da tasan ko waye angon ba
saboda tasan ba zabinta bane zabin iyaye ne
(sunan wani littafi na hafsata bounzer) dan haka
kawai hidimar gabanta takeyi. Abangaren lamin
kuwa yafi kowa murna da sanya wannan rana,
tuni ya koma kano yaje ya dora daga inda ya
tsaya wannan karon Angelina da blessing ne
suka je gidan nasa amma kullum cikin fada suke
da zarar ya fita zasu fara dambe ganin haka
yasa ya tattarasu yakora yayiwa Mary waya
yace tazo.
[3/22, 4:39 PM] Ummi A'isha🏻: MACE GUDA

DAYA TILO...ƒ£2⃣

Na
UMMI A'ISHA
Biki ya rage saura sati 2 lamin ya shirya
shida yayansa sukaje bauchi domin gaisheda
iyayen junada ita kuwa lokacin bama ta kasar
sun tafi sudan itada kanwar mahaifiyarta mami
inda za ayi mata gyaran jiki da sauran abubuwa
na amare kuma bazasu dawo ba sai ana saura 3
days biki,cike da girmamawa da mutuntawa su
lamin suka gaisa da kowa lfy sannan suka koma
yola inda acanma shirye shiryen bikin ake tayi
dan har an harhada lefe aranar aka kai na matar
abdulrahman mai suna kausar yar gidan sarkin
yola ce yayinda na junada akace sai washe gari.
Hakan kuwa akayi washe gari yan kaiwa kaya
suka nufi bauchi kayane na kece raini akwati 24
set daya brown daya set din kuma pink colour
yan uwan junada sunyi mutukar murna hakan
nema yasa suka bada tukwici na naira dubu dari
biyu. Tunda biki ya rage saura kwana 8 gidansu
lamin suka fara shirye shiryen komawa sabon
gida domin acanne za a gudanar da bikin, wani
tangamemen gida state government ta ginawa
mahaifinsu akusada government house gidan
unguwa gudane domin part guda 5 ne acikin
gidan dan haka ananma su lamin din zasu
zauna.
[3/22, 4:40 PM] Ummi A'isha🏻: MACE GUDA

DAYA TILO..ƒ£3⃣

Na
UMMI A'ISHA
Ana saura kwana 3 biki su junada suka dawo
daga Sudan tasha gyara tayi tsananin kyau sai
sheki da kyalli take tamkar wata tauraruwa,
gaba daya ta yi wata kala ga uwar rama datayi
saboda bata iya cin abinci. Shi kuwa lamin
baima yi gayya ba domin acewarsa wannan ba
biki zaiyi ba zaiyi bikinsa sai nan gaba yanzu
bai isa aureba, ana igobe za afara shagalin biki
suka koma sabon gidansu anan aka fara
gudanar da biki washe gari akaje aka daura
auren Abdulrahman da Kausar sannan aka wuce
garin bauchi inda jama'a sukayi dafifi domin
jiran daurin auren, ango yayi kyau cikin wata
shudiyar shadda wadda tasha dinki mai tsadar
gaske 12 dai dai aka daura auren junada
mukhtar da angonta Lamin Kabir sulaiman akan
sadaki dubu dari, ana daura auren lamin yayi
tafiyarsa batare da ya nemi ganin amaryar ba.
Ita kuwa dama ko sha'awar ganin fuskarsa
batayi domin batasan waye ba kuma bata son
tasanshi haka aka wuni ana kade kade da raye
raye gamida bushe bushe yamma tanayi aka
dauki amarya sai garin yola inda aka kaita
dakinta.
[3/22, 4:42 PM] Ummi A'isha🏻: MACE GUDA

DAYA TILO..ƒ£4⃣

Na
UMMI A'ISHA
Wurin iyayen mijinta aka fara kaita sannan
aka nufi sashenta da ita. Bayan kowa ya tafi ne
husna da hasna suka shigo dakin nata idonta
jajur kamar barkono tafara kallonsu dam taji
gabanta yafadi domin sunyi mutukar yi mata
kama da wannan copper din zama sukayi akusa
da ita suka fara zuba mata surutu kallo ita dai
take binsu dashi acikin ranta tana fadin waw
identical twins dan hatta muryarsu iri dayace
komai nasu iri daya babu ta inda suka banbanta,
basu suka bar side dinta ba sai 10 nadare ita
kuwa zaune tayi tana ta faman kuka shiru shiru
babu ango babu dalilinsa har bacci ya dauketa.
Karfe 6 ta tashi tashiga tayi wanka ta shirya
cikin wata atamfa super purple colour dinkin
bubu yayi mutukar amsarta, window din dakinta
ta leka girman fadin tsakar gidan ne yaso
tsoratata don babbane sosai part biyar tagani
duk iri daya daga can gaba katon filin wasa ne
an sassaka kayan motsa jiki ga wurin basketball
da volleyball nan daga gaba kuma wurin table
tannins ne komai dai na wasa an tanada awurin
window din tasaki takoma na daya bangaren ta
daga wani katon swimming poll ta hango gaba
dashi kuma garden ne kawatacce.
[3/22, 4:44 PM] Ummi A'isha🏻: MACE GUDA

DAYA TILOƒ£5⃣

Na
UMMI A'ISHA
Dakin nata tabi da kallo yasha furnitures
masu tsada komai red da ratsin baki fitowa
daga cikin dakin tayi wani dakin tagani yana
kallon nata tsakiyarsu kuma dan karamin falo ne
shima tunda ga kujerun zuwa labulayen duk red
and black ne ga madaidaiciyar plasma tv manne
ajikin bango, dakin dayake kallon nata ta bude
tashiga shima babu laifi ya kawatu mutuka da
kaya irin na zamani komai naciki red colour ne
da toilet aciki fitowa daga ciki tayi ta murda
kofar falon wani tangamemen falo tagani wanda
ya sha luntsuma luntsuman kujeru har kala biyu
daya ash colour dayan kuma pink colour ne dan
haka labulayen ma sai suka kasance pink da
ash colour ga wata jibgegiyar plasma manne
abangon falon daga gaba kadan dining area ne
taciki ga kitchen nan da store agefe, gefenta ta
kalla shima dai wata kofar ce da alama shima
irin dakunanta ne da dan falo aciki ma'ana dai
sun saka tangamemen falon a tsakiya sukuma
suna facing din juna dan haka shima ji tayi tana
sha'awar ganin yanda aka tsarashi da karfin
gwiwarta ta murda kofar tashiga dan karamin
falo ne kamar nata da kujeru light green kanta
ta daga tafara bin hotunan dake manne ajikin
bangon falon da kallo cak! Taji numfashinta ya
tsaya sakamakon ganinsa da tayi ajikin
tangamemen hoton yana sanye da bakar riga ya
gyara sumarsa yana murmushi.
[3/23, 9:51 AM] Ummi A'isha🏻: [3/23, 9:21 AM]
Ummi A'isha🏻: MACE GUDA DAYA TILO
ƒ£6⃣

Na
UMMI A'ISHA
Idanuwansa manya farare tatas kamar an
diga zaiba aciki babu abinda yafi burgeta irin
jajayen lips dinsa yayi bala'in yimata kyau sosai
dadine ya kamata azuciyarta tafara fadin ya
Allah kasa ba gizo wannan bawan naka yake
min ba Allah kasa dagaske shine abokin
rayuwata na har abada,sallamar da ta jiyo a
babban falone yasata saurin fita daga cikin falon
nasa hasna da husna tagani dauke da kayan
breakfast sunsha ado sosai dasauri ta taresu
tana fara'a a'a yan biyune sukazo sannunku da
zuwa hasna ce tace sannu matar yaya ranta fari
tas tazauna dasu suka fara hira har azahar tayi
sannan suka bar side din nata suka koma nasu
shiru shiru bata ga ango ba da haka har akayi
kwana 5 da bikinsu sai dai kullum su hasna
nazuwa su tayata hira wuni sukeyi awurinta
wani lokacinma har dare suke kaiwa, yau tunda
safe tafito babban falon ta zauna sallamar wata
yar kyakkyawar mace taji ta amsa mata tashigo
ciki bayan sun gaisa tace mata Kausar ce matar
Abdul brother din lamin murmushi tayi tace
sannu da zuwa yau kin fito kenan itama
murmushin tayi tace eh yanzuma sallama nazo
miki zamu tafi Uganda ne nida shi shiyasa nace
baxan tafiba sai nashigo munga juna mikewa
tayi tace yana waje yana jirana dan har mun fito
itama mikewar tayi tabi bayanta tana cewa Allah
ya saukeku lfy.
MACE GUDA DAYA👆TILO
2⃣7⃣

Na
UMMI A'ISHA
Suna fita tsakar gida ta hangoshi gabanta
yayi mummunar faduwa ahaka suka karasa inda
suke tsaye suna jiransu sai da sukaje daf dasu
sannan taga ashe ba mijinta bane sai dai suna
mutukar kama sosai amma mijinta yafishi kyau
nesa ba kusa ba kuma yafishi fari russunawa
tayi ta gaida shi cikin sakin fuska ya amsa su
husna ne suka runtumo suka zo suka rungumeta
suna dariya itama dariyar tafara yi musu
sallama sukayi dasu Kausar suka tafi ita kuma
su hasna tabi side din mummy yaune karo na
farko da ta fito tun zuwanta gidan side din
mummy irin nata ne sak,adaki ta taradda ita ta
sunkuya har kasa ta gaida ta amsa cikin kulawa
sannan tace ai mijin naki yace gobe zai dawo
daga kanon ko? Dam tayi sannan tace ehh dan
bata son mummy ta fahinci har yau bata ganshi
ba mummyn ce taci gaba da cewa jiya nake
cewa aturo miki masu aiki guda uku da mai
shara da wanke wanke da mai girki sai mai
wanki shine lamin yace ai kince baki bukata zaki
nayi duk da kanki kuma bakida ra'ayinsu
shiyasa ma bakiyi magana ba kanta ta daga
tace eh ninace kar akawo itadai mummy
mamakine ya cikata saboda daga ganin wannan
yarinyar kasan yar hutuce babu wahala atare da
ita amma tunda ita tace bata ra'ayi shikenan
mikewa tayi ta shiga dakin su husna nanfa suka
fara hira babu laifi ta saba dasu dan haka ta
sake dasu sosai fiyeda mummy domin tana dan
jin nauyinta anan ta wuni har yamma sai da
la'asar lis sannan suka dunguma suka koma
bangarenta sai wurin goma sukayi mata sallama
suka tafi.
MACE GUDA DAYA TILO
ƒ£8⃣

Na
UMMI A'ISHA
Yau a lissafinta kwanasu 10 da aure amma
bata taba dora idonta akan mijinta ba kullum ita
take yin aikinta shara wanke wanke girkine ake
kawo mata daga wurin mummy kullum acan
take wuni sai dare take dawowa side dinta.
Wanka tayi taci kwalliya cikin wani material ja
tafito da niyyar taje wurin mummy tana fitowa
ta hango wata sabuwar mota blue kirar
Mercedes 2015 new model tana shigowa tana
karasowa ciki akaje akayi packing dinta a
garage ya bude ya fito yana sanye cikin bakar
riga an zana stars guda uku ajiki an rubuta just
bring it ajiki yasa bakin wando yayi mutukar
kyau fuska adaure ya karaso inda take yace ina
zaki? Wata irin faduwa taji gabanta yayi yayin
da zuciyarta ke dukan uku uku ba kakkautawa
wurin mummy zani to muje ciki ina son magana
dake yafada yana ta faman huci sim sim ta
wuce yana biye da ita har cikin babban falon
kujera ya samu ya zauna yayinda ita kuma ta
zauna can nesa dashi kallo yabita dashi sannan
yace ke! Karkiyi tunanin ko na aureki ne dan kin
burgeni ko dan ina sonki no na aureki ne domin
na wulakanta ki na nuna miki ke ba kowa bace
face baiwa dan awurina baki da maraba da
kuyanga zan maida ke tamkar baiwa wadda
zata zama abin kwatance agari nine nan na
hana mummy ta kawo miki yan aiki saboda
wannan yana daya daga cikin horon da zanyi
miki acikin gidan nan saina gama azabtar dake
sannan zanyi miki saki uku kwarara yanda zaki
dade kina jin bakin ciki arayuwarki, daga yau
kece zaki nayin duk wani aiki nawa kama daga
abinci wankin kayana gyaran dakina da sauran
ayyuka kuma wlh koda wasa kika fadawa
mummy saina raunata ki banza kawai ki kalleni
da kyau ni ba class dinki bane wlh level dina ya
wuce naki.
[3/23, 9:25 AM] Ummi A'isha🏻: MACE GUDA

DAYA TILOƒ£9⃣

Na
UMMI A'ISHA
Tunda yafara bayaninsa binsa kawai take da
ido batare da tayi koda motsi ba har ya diga aya
wani mugun kallo ya watsa mata yace kalleta
kamar mutuniyar kirki mai kamada aljana kawai
sannan magana ta karshe duk abinda kika gani
adakina kar ki kuskura ki taba mun ki bar min a
mazauninsa idan kuma ba hakaba zaki yabawa
aya zakinta dan sai jikinki ya gaya miki wlh
yana kaiwa nan ya mike ya shige dakinsa ita
kuwa ta kasa koda motsi dan fargabar irin
zaman da zatayi dashi sai dai ita kuma har
acikin ranta taji tana tsananin sonsa sannan
kuma yana burgeta tun ranar farko data fara
ganinsa ta dade azaune sannan ta tashi ta shiga
kitchen ta dora abinci akaro na farko tun
zuwanta gidan domin kullum mummy ce take
bayarwa ake kawo mata shinkafa da miya ta
dafa sa'arta daya ta iya girki domin ko agida
wani lokacin itace take yiwa abbansu girki
musamman ma idan zaiyi baki na kunya haka ta
shirya abincinta mai rai da lafiya taje ta jera
akan dining sannan ta wuce dakinta har yanzu
bata jin zafin sa sai dai abu dayane ya tsaya
mata arai auren ramuwar gayyar da yayi da ita
shine har yanzu yake damunta tana daga cikin
dakinta ta jiyoshi yana waya amma ba zata
tantance da mace yakeyi ko da namiji ba abincin
ya danci kadan sannan ya wuce side din
mummy tundaga babban falo ya fara jiyo
muryarsu husna suna cewa wlh mummy yaya
lamin yafi yaya Abdul iya zabe matarsa tafi Anty
Kausar kyau daya daga cikinsu yaji tana cewa to
danma ba kiga gashinta ba ni jiya dana shiga
dakinta lokacin ta fito daga wanka tsorata nayi
gashinta fa har kugunta yanda kika san yar
India murmushi momyn tayi tace ai dama daga
ganinta zatayi gashi dai dai lokacin ya shiga
cikin falon mummy suna ganinsa sukayi tsit sim
sim suka fara kokarin fita suna cewa sannu da
zuwa yaya lamin side din junada suka nufa suna
fadin umm su anty junada yau honey ya dawo.
MACE GUDA DAYA TILO
ƒ£0⃣

Na
UMMI A'ISHA
Suna shiga suka sameta zaune acikin falonta
tana kallon wani Nigerian film a tashar
Nollywood zama sukayi suka fara tsokanarta
yau anty junada ko nemanmu ba kyayi saboda
yaya yadawo ko? Murmushi tayi tace ku kuka
sani dai hasna ce tace wai anty junada ke yaya
yana yimiki dariya husna ce tayi tsagal tace ba
dolensa ba ita dai bata tanka musu ba haka
suka karaci surutunsu nan suka zauna har
magriba sai da sukaji shigowarsa sannan suka
bar bangaren nata suka nufi nasu. Haka
zamansu ya kasance Ita dashi kullum tana shiga
tana gyara masa daki yauma kamar kullum tana
jin fitarsa ta nufi dakinsa tashiga da toilet tafara
sai da wankeshi tas sannan ta dawo cikin dakin
tafara gyarawa ta shareshi tas ta goge tile din
ta fito da kananan kayansa ta wankesu sannan
ta fesa air freshener adakin drawer mudubinsa
ta jawo tana shirya masa wasu takardu da
tagani ya barbaza akan gado da alama test
yayiwa dalibansa shine da yagama marking ya
bazasu anan yatashi ya barsu awurin tana gama
shiryasu kamar ance buda ta kasan ta jawo ta
bude me zata gani wani kwali tagani yanata
kyalli ta dauko tana budawa taga sun zubo tana
duba jikin kwalin taga an rubuta condom
gabanta ne yafara faduwa dasauri ta mayar
masa inda yake ta ajiye ta rufe drawer ta koma
dakinta innalillahi kawai take fada ba dai lamin
neman mata yake yi ba? Tambayar da take ta
yiwa kanta kenan innalillahi wa inna ilaihi raji'un
zina? Kukane ya subuce mata nan ta zauna ta
sha kukanta ta more wani kishine ya turnuke ta
ganin kukan bashine mafita ba yasa ta tashi
tashiga bathroom ta wanke fuskarta ta fito ta
tsaya agaban mudubi ta gyara fuskarta fes ta
fito ta nufi side din mummy tana shiga ta hango
shi a babban falon yana kishingide yana karanta
jarida ta gabanshi tabi ta wuce tashiga falon
mummy ta samesu zaune ita dasu hasna suna
ganinta suka fara murna oyoyo antynmu yanzu
muke cewa bari mu tashi muzo tunda ke baki
shigo ba har yanzu.
[3/23, 9:51 AM] Ummi A'isha🏻: [3/23, 9:29 AM]
Ummi A'isha🏻: MACE GUDA DAYA TILO
ƒ£1⃣

Na
UMMI A'ISHA
Murmushi tayi sannan tace ku dai kuyi shiru
kawai tunda gashi na zo shikenan ta durkusa
tana gaida mummy sannan suka dunguma zuwa
dakinsu su husna anan suka zauna suka fara
hira sai da rana tayi sannan tafito mummy ta
hango tana kokarin shiga kitchen ta dora girki da
sauri ta bita tace mummy me za adora? Cike da
jin dadi tace jalop rice zan dafa to mummy
barshi zan dafa cikin jin dadi mummyn tace to
Allah yayi miki albarka ta juya ta fita daga cikin
kitchen din cike da jin dadin yadda junada take
darajata kuma take mutunta ta a falo ta zauna
wurin lamin tanata yabon junada kafin kace me
tuni junada tagama girkin ta yi farfesun hanta
sannan ta hada salad ta zuzzuba su a flasks ta
zo ta jera akan dining farin ciki ne ya mamaye
zuciyar mummy, dakin su husna takoma ta
zauna suka ci gaba da caftarsu ba ita ta tafiba
sai dare tana zuwa dakinta ta sawa kofarta key
ta kwanta nan da nan taji bakin ciki ya
mamayeta sakamakon tunowa da abinda tagani
adakin lamin wata zuciyar tace yanzu har ya isa
neman mata? Eh ya isa mana tunda rayuwar
waje yayi wata zuciyar ta bata amsa dakyar ta
samu bacci ya dauketa. Ahaka suka zauna har
ya gama weekend dinsa ya koma kano, kullum
dakin su husna take wuni idan lokacin girki yayi
ita zata shiga ta girka musu, suna jin dadin
zama da ita sosai itama tana jin dadin zama
dasu mutuka gashi kuma shi kanshi dadyn nasu
yana ji da ita dan yauma foam ya kawo musu
na federal university Yola yace su cike su ukun
zasu fara zuwa makaranta tare. Su hasna
psychology suka cike ita kuma micro Biology
zata karanta,shi kuwa lamin yana can kano yana
shagalinsa yama manta da wata junada tunda
yatafi bai dawo ba saida yayi 2 weeks sannan
yazo amma duk da haka junada bataji zafinsa
ba asalima Allah Allah take yazo ta ganshi tana
cikin dakinsa tana goge masa takalmansa ya
shigo ko kallonta baiyi ba ya ajiye jakarsa ya
shiga bathroom, murmushi tayi ta tashi tafita
domin ta hada masa abinda zai ci.
MACE GUDA DAYA TILO
ƒ£2⃣

Na
UMMI A'ISHA
Taliya da macaroni ta dafa masa da miyar
kwai ta kawo masa kan dining sannan ta fita
zuwa bangaren mummy, yana fitowa daga
wanka ya shirya cikin jar riga da wando baki
yafesa turaren volish mai sanyin kamshi ya fito
falo abincin data ajiye masa yaje ya buda
kamshi ne ya bugeshi domin miyar tun a ido ta
burgeshi tayi yellow tasha curry zama yayi ya
zuba yaci ya koshi sannan ya fita wurin mummy
acan ya samesu sunata zuba a babban falo
amma suna ganinsa suka yi shiru bai kulasu ba
ya shigewarsa dakin mummy. Sai dare yauma
takoma side din ta lokacin data shiga yana
zaune a babban falo yana daddana laptop
dagowa yayi ya kalleta yace ke kawo min tea to
ta amsa ta shiga kitchen ta hado masa tazo ta
ajiye akan dan teburin dake gabansa ta wuce
dakinta. Dasafe ta tashi ta gyara ko ina tsaf ta
shiya breakfast sannan ta wuce dakinsa baya
ciki da alama ya fita gyara dakin tayi sannan ta
debo kayansa data wanke masa tun jiya tafara
gogewa tana cikin gugar yashigo ya wuceta
yashiga wanka bai dade sosai ba ya fito daga
shi sai gajeren wando kallo daya tayi masa ta
sunkuyar da kanta kasa ke ina kika ajiye min
pants dina da kika wanke min? Mikewa tayi
cikeda jin kunya ta dauko masa ta bashi warta
yayi sannan ya wuce gaban drawer yafara
shiryawa.
[3/23, 9:31 AM] Ummi A'isha🏻: MACE GUDA

DAYA TILOƒ£3⃣

Na
UMMI A'ISHA
Kanta yana sunkuye har yagama shiryawa
yafita daga cikin dakin gugar taci gaba dayi har
ta goge kayan tas gaba daya ta fito ta shiga
dakinta tayi wanka tana fitowa ta jiyo hayaniyar
su hasna acikin falonta ta shirya ta fito wurinsu.
Ranar Monday da sassafe ya fice ya nufi kano
ita kuma ta tafi wurinsu mummy tana shiga
suka fara yi mata albashir da sun samu
admission har daddy yasa aje ayi musu
registration dadi taji domin ko ba komai karatun
zai dan debe mata kewa,aranar ummanta tazo
mata murna kamar zatayi ihu haka suka koma
side dinta ta cikata da kayan ciye ciye ita kuwa
mahaifiyar tata kallon yartata takeyi tare da son
jin irin zaman da sukeyi da mutanen gidan cikin
fara'a tace wlh umma zamanmu lafiya dasu
kowa yana kaffa kaffa dani harta shi kanshi
daddy bakiga yadda yake kaunata ba kuma shi
baima cika zama agida ba amma duk lokacin da
yayo waya sai ya tambayi lafiyata dadi umman
taji sannan tace to ya zamanku da mijin naki
kuma? Murmushi nanma tayi tace shima lafiya
lau muke zamanmu umma yau da sassafe ya
tafi kano cikin fara'a tace ai mijinki yaron kirki
ne last week ma yaje ya gaishe mu, amma ina
masu aikin naki naga kamar babu kowa? Kanta
ta daga eh wlh umma mummy ta samo min
guda 3 to gaskiya banida ra'ayi ne tunda aikin
nawa ba wani mai yawa bane kuma ni in banda
kwanciya babu abinda nakeyi shiyasa nace gara
kawai na rinka aikin mijina da kaina ko nafi
samun lada murmushi umman tata tayi tace
dakyau gaskiya kinyi kykkyawan tunani Allah
yavada lada haka suka ci gaba da hirarsu batare
da umman ta fahimci akwai matsala tsakaninta
da mijin nata ba, wuni guda umman tata tayi
amma ko kadan bata fahinci akwai matsala da
mijin nata ba sai la'asar sannan sukayi mata
rakiya zuwa airport ta hau jirgi ta tafi bauchi.
[3/23, 9:35 AM] Ummi A'isha🏻: MACE GUDA

DAYA TILOƒ£4⃣

Na
UMMI A'ISHA
Acikin satin aka gama musu registration da
komai na makaranta dama tuni anfara lectures
dan haka daddy yace next week sai su fara
zuwa da kansa ya dauko key din mota sabuwa
Benz C230 ya bata yace saboda zuwa
makaranta murna wurinsu ba acewa komai ita
kanta junadan murna take domin ta daura
aniyar karatun dagaske bada wasa ba,shi kuwa
lamin ko weekend dinma bai zo ba saboda yana
can tareda Mary a kano haka yayi zamansa bai
waiwayi yola ba. Ranar Monday suka fara
halarta makarantar su uku husna da hasna
department dinsu daya ita kadai ce department
dinta daban haka suka rinka zuwa wani lokacin
har 2 suke kaiwa a makaranta babu laifi yanzu
tana dan samun saukin tunanin da yaje
addabarta. Sai karshen week din lamin yazo
yola lokacin tana side din mummy suna kallon
wani Indian film mai suna fashion kallo ya bisu
dashi yace kullum Ku kenan a kallo kun shiga
makarantar ma amma bazaku rage kallo ba
maza dai yarinya ta samo carry over wlh saina
tattakata sai a sannan junada ta daga kai ta
kalleshi yana sanye da brown din riga da bakin
wando fuskarsa sai sheki take tamkar wani
tauraro bataso ya daina yi musu fadanba domin
tana son amon muryarsa tana yimata dadi sosai
dakin mummy ya shigewarsa husna kuwa taba
baki tayi tace kaji shi ko ina ruwansa itama
hasna bakin ta taba tace bar masifaffe kawai ai
kuwa nan da nan junada ta bata fuska tace
bana son cin fuska gaskiya ya kuke zagin mijina
agabana? Murmushi sukayi sorry Anty harda
hada baki hakan da sukayine ya bata dariya
sosai. A haka sukaci gaba da zama har
karatunsu yayi nisa alokacin shi kuma lamin ya
gama service dinsa ya tafi Malaysia ya karbo
result dinsa yana dawowa ya samu aiki a state
university yola yafara lecturing tsakanunsa da
matarsa kuwa sai dai kallo domin har yanzu
yana nan akan bakansa neman mata kuwa
yanzu ma yasa kafa.
Duniyar makaranta littattafan Hausa
Group Admin
MACE GUDA DAYA TILO
ƒ£5⃣

Na
UMMI A'ISHA
Haka suka ci gaba da zaman doya da manja
tsakaninta dashi kullum side din mummy take
wuni idan babu makaranta idan da akwai kuwa
tana dawowa acan zasu yada zango ita dasu
hasna sai dai kullum tana gyara masa dakinsa
ta wanke masa toilet ta wanke masa kayansa ta
dafa masa abinci ta ajiye masa amma bata taba
burgeshi ba asalima shi a matsayin yar aikinsa
ya ajiyeta. Semester tayi nisa domin har sun kai
middle karatu sukeyi sosai kuma acikin wannan
yanayin ne daddy da mummy suka samu visa
zasu tafi kasar Spain inda daddy din zai halacci
wani workshop na tsawon sati biyu daga nan
kuma zasu wuce saudiyya domin gabatar da
umara dan haka tuni suka fara shirye shiryen
tafiya su kuma su husna sun gama hado
kayansu sun dawo sashen junada,washe gari
sukayi sallama dasu suka tafi suna tafiya suka
dawo falon junada suka zauna suna hangowa
yadda zasu kwashe da zaman gidan yaya lamin
ai kuwa basu dade da zama ba sai gashi fuska
babu annuri ya shigo ya ce ina take? Tana daki
husna ta bashi amsa to kice ta kawo min abinci
ya wuce dakinsa tashi husna tayi tashiga dakin
lokacin ita kuma junada tagama shiryawa cikin
wata atamfa yellow dinkin riga da skirt husna
tayi murmushi kin gama adai dai anty domin
yanzu yaya yadawo yace ki kai masa abinci to
ta amsa tafita da sauri tashiga kitchen dambun
shinkafa tayi da farfesun koda ta dauki juice mai
sanyi ta nufi dakin nasa yana zaune bakin gado
daga shi sai gajeren wando yana waya kanta a
kasa ta isa gabansa ta ajiye farantin ta juya ta
fice. Suna nan zaune a falon yafito cikin shiga
mai kyau blue din jeans da pink din riga yayi
kyau sosai sai kamshin turaren Phoenix ne ke
tashi ajikinsa ko inda suke bai kalla ba yafice.
[3/23, 9:51 AM] Ummi A'isha: [3/23, 9:41 AM]
Ummi A'isha🏻: MACE GUDA DAYA TILO
ƒ£6⃣

Na
UMMI A'ISHA
Husna ce ta kalli hasna tace tofa ai mun shiga
uku kuma tunda aka barmu awurin wannan
mugun hasna tace ai dama wlh da yaya Abdul
na nan agidansa zamu zauna harararsu junada
tayi tace ai kuwa da baku isaba wlh suna cikin
maganar sai gashi sun shigo shida wasu mata
guda 2 kyawawa dakinsa suka wuce bako sannu
dama yan matan ba musulmai bane Jim kadan
sai gashi ya fito ya kallesu daya bayan daya
yace wadannan abokan aiki nane zasu zauna
anan dan haka wlh koda wasa naji yarinya ta
fada idan su daddy suka dawo sai na illata ta
kuna jina kai suka daga dan duk cikinsu babu
wacce ta iya magana junada kuwa tafi kowa
bakin ciki ranta ya gama baci sosai juyawa yayi
ya koma dakin hasna ce ta mike ta shiga
dakinsu wanda yake opposite din dakin junada
husna itama tashi tayi tabi bayanta tana shiga
tasameta ta rafka tagumi kusa da ita taje ta
zauna tace hasna me kika fuskanta da wannan
lamari? Cikin takaici hasna tace ai husna yaya
lamin dan rainin wayone wai abokan aiki
wadannan sunyi kama da lecturers? Kawai yan
matansa ne wlh ni dama nadade da sanin yaya
lamin yana neman mata cikin bacin rai husna
tace ai shiyasa kullum nake tausayawa anty
junada tana mutukar hakuri dashi kuma bata
taba nuna mana laifinsa ba kullum cikin boye
sirrinsa takeyi bata taba fada mana tsakaninsu
ba Allah shiryeshi amin inji husna. Ita kuwa
junada dakyar ta iya tashi saboda jirin da yake
dibanta sai yau tasan tana tsananin kishin
mijinta akan gadonta ta kwanta tafara wani irin
kuka mai ban tausayi acikin zuciyarta kuwa
addu'a take masa Allah ya shiryar dashi haka ta
wuni tana kuka tuni kanta yafara ciwo amma
haka ta fito ta shiga kitchen ta dafa musu abinci
ta koma dakinta ranar haka dukansu su ukun
suka wuni cikin takaici shi kuwa yana can yana
holewarsa.
MACE GUDA DAYA TILO
ƒ£7⃣

Na
UMMIA'ISHA
Wasa wasa tun abin yana basu haushi har ya
dawo ya daina basu domin yan matan nan sai
da suka shafe kwana 9 acikin gidan sannan
suka tafi shi kuwa ko ajikinsa su husna kuwa
basu isa sun fadi laifinsa agaban junada ba dan
yanzu zata bata rai taji haushinsu sai dai idan
sun koma gefe suyita Allah wadai da halin yayan
nasu ita kuwa junada addu'a kawai take yi Allah
ya shirya mata shi ya karkato mata da
hankalinsa kanta. Ranar Monday tunda wuri ta
tashi ta shirya masa breakfast ta gyara masa
dakin ta koma ta tashi su husna suka shirya
suka tafi makaranta suna dawowa suka tarar
yana fitowa shida wata farar budurwa Christian
da sauri suka basu hanya suka fita sannan suka
shiga falon,junada cikin ranta taji kamar taje ta
shake wannan matar amma babu dama. Aranar
da daddare yazo da wata daban shi kuma
sassafe ya fice domin 8 to 10 yake yiwa wasu
daliban lecture wasu kuma 1 to 2 ita kuwa
junada saida tagama gyara ko ina sannan ta
nufi dakin nasa da nufin gyarawa tana shiga ta
ganta kwance kyakkyawa ce sosai ai nan da nan
kishi ya cikata duka ta daka mata firgigit ta
tashi tana mikewa ta kifa mata mari tace dan
ubanki me ya hadaki da mijina tsorone ya kama
arniyar tace kiyi hakuri bai cemin yana da mata
ba, ni nafada miki kuma yau sai na kasheki wata
kwalbar lemo ta dauka tace zaki kara kula
mijina? Cikin tsoro tace a'a hakuri ta fara bata
sosai saida ta Kara wanketa da mari sannan ta
hankadata waje ta cilla mata jakarta waje ai tuni
tafice daga gidan aguje ranta babu dadi tagama
gyara dakin tafice. Haka zaman nasu ya
kasance har sati 3 tuni an kafe musu time table
na exam anyi closing lectures din dan haka babu
inda suke zuwa karatu kawai sukeyi agida.
[3/23, 9:47 AM] Ummi A'isha🏻: MACE GUDA

DAYA TILO..ƒ£8⃣

Na
UMMI A'ISHA
Yauma kamar kullum da sassafe junada ta
tashi tagama gyare gyaren gidan su husna suna
can suna aikin nasu wato bacci idan suka
kwanta bacci daga asuba sai sun Kai 12 basu
farka ba itace take tashi da wuri take ayyukanta
duka. Wurin 11 tagama komai ta shiga dakinsa
baya ciki da alama ya fita kananan kayansa ta
tattara tashiga toilet ta wanwanke sannan ta
wanke toilet din, tana gamawa tadawo cikin
dakin tafara gyarashi tana gyaran gado suka
shigo shida wata arniya siririya baka kyakkyawa
ya dan saci kallon junadan yaga tayi kicicin
kunya ya dan ji don baisan tana cikin dakin ba
kallon yarinyar yayi yace Jen have a sit am
coming ficewa yayi daga dakin Jim kadan sukaji
karar tashin motar da alama fita yayi daga
gidan juyowa junada tayi taga karuwar tasa tana
gyara fuskarta ajikin mudubi fisgo ta tayi tafara
wanka mata mari tas! Tas! Tas tace dan ubanki
zaki kara biyo mijina? Cikin kuka tace no am
sorry pls tace ba wani hakuri dan ubanki yau
saina datse miki kafafu tuni Jen ta rude tafara
bata hakuri fincikarta tayi ta hada da bango ta
shaketa dai dai nan yashigo dasauri junada ta
saketa ita kuwa tace kafa me naci ban baki ba
sai gudu ko sauraronsa batayiba, cike da
mamaki ya kalli junada yace me kikayi mata?
Shiru tayi masa taci gaba da aikinta ransa ya
baci sosai ficewa yayi daga dakin ya koma falon
ya zauna ita kuwa aikinta tayi tana gamawa ta
fito ta wuce dakinta.
MACE GUDA DAYA TILO...
ƒ£9⃣

Na
UMMI A'ISHA
Mamaki ne ya kamashi to me yakori jen?
Wayarsa ya dauka yafara kiranta tana dauka
tafara zaginsa tana cewa banza mayaudari
dama ashe kanada mata shine ka daukeni ka
kaini gidanka dan matarka ta kasheni ko? To
daga yau babu ni babu kai macuci kawai ta
kashe wayarta mamaki ne ya cikashi to me
wannan yarinyar take nufi? Rannan ma da
yadawo bai samu Grace ba bayan kuma yatafi
ya barta adakin da yakirata awaya da kyar ta
dauka ta zazzageshi wai ba ita bashi domin
matarsa mahaukaciya ce kashe mutane take
wato itace take korarsu kenan kodai sonsa take?
Tashi yayi yabar falon ganin bashida amsar
tambayar da yayiwa kansa. Ita kuwa ta daina
ma saka abun aranta addu'a kawai takeyi Allah
ya shirya shi, yau saura kwana 3 su mummy su
dawo daga umara har sun fara shirye shiryen
taryarsu tana dakinta akwance su husna kuma
suna daya dakin ya shigo ki tashi ki dafa min
indomie guda 4 da soyayyen kwai ki kawo min
daki to tace ta mike ta shiga kitchen tana
mamakin kanta wai yau itace ake juyawa haka
duk irin gatan ta lallai ta yadda sarki agidan
wani sarkin bawa ne da wannan tunanin ta
gama dafawa ta soya kwai guda 6 ta dauki
cokala guda biyu dan tasan shi kadai indomie
Hudu tayi masa yawa dan bashida cin abincin
sosai dakin nasa ta nufa ta kwankwasa shiru
dan haka kawai sai ta tura kofar tana shiga ta
hangoshi daga shi sai gajeren wando ita kuwa
karuwar tasa zigidir take haihuwar uwarta sun
shagala sai romancing juna suke tuni jikinta ya
fara rawa ta saki farantin abincin ya zube filet
din tangaram din ya fashe karar ce tadawo dasu
cikin hankalinsu tuni ta ruga aguje tabar dakin
shi kuwa jikinsa yaji yayi masifar sanyi rana ta
farko da yaji kunyar junada ranar farko da yaji
ya tsani zina arayuwarsa kuma yaji ta fita acikin
ransa tashi yayi yace da Agnes ta shirya ta bar
gidan tambayarsa abinda ya faru tafara wata
tsawa ya daka mata yace ta fice kawai cikin
sauri ta shirya ta dauki jakarta ta fita shi kuwa
kamar wanda aka zarewa laka ajiki duk ya
sukurkurce.
Duniyar makaranta littattafan Hausa Group
Admin
Ummi A'isha
MACE GUDA DAYA TILO..
ƒ£0⃣

Na
UMMI A'ISHA
Tana isa dakinta ta kwanta akan gado jikinta
sai faman rawa yake innalillahi kawai take
ambata, hayaniyar su husna ta jiyo a falo amma
bata fita ba tana nan kwance kamar marar
lafiya, shi kuwa lamin dakyar ya iya tashi yasa
kayansa ya fito daga falo tajiyo yana tambayar
su hasna ina take? Tana cikin daki inji su kai
tsaye dakin ya wuce ya ganta kwance ta
kudundune kanta ke ki tashi kije ki gyara min
dakina da kika bata ni fita zanyi yana fadin haka
ya fita ita kuma tashi tayi tana mamakin shi
kuwa lamin me yagani ajikin wannan arniyar? In
banda kashi ita bata ga komai ajikinta ba amma
dan jaraba irin ta maza shi burgeshi tayi ahaka
mikewa tayi taje ta gyara dakin ta kunna turaren
wuta sannan ta rufo kofar ta dawo wajen su
hasna. Washe gari da wuri ta fito saboda
yunwar da takeji kanta tsaye kitchen ta wuce ta
debo ruwan zafi tazo ta hada tea mai kauri ta
dawo falo tafara sha da niyyar idan ta gama
zata koma kitchen ta hadawa su hasna da lamin
nasu, kamshin turarensa tafara jiyowa tuni
kamshin nasa ya gama rudata ta ajiye kofin
sakamakon ganinsa da tayi ya fito yana sanye
cikin suit bakake yayi kyau sosai kallonta ya yi
sannan yace bani breakfast dina fita office zanyi
dasauri ta mike ta shiga kitchen ta soya masa
manyan kwai guda 4 ta debo ruwan zafi a kofi
sannan ta dauko masa bread ta dawo ta ajiye
masa ta koma ta dauko butter da yar wukar da
za ashafa butter din ta dawo ta ajiye ta nufi
kitchen ke ni zan shafa butter din? Taji yace
dawowa tayi tazo ta tsugunna ta dauka ta fara
shafa masa shi kuma ya dauki kwan ya fara ci,
yan yatsun hannunta ya zubawa ido farare sol
dasu dogaye miko masa tayi yasa hannu ya
karba yana mai ci gaba da kallon hannun nata
tana gamawa ta mike ta koma kitchen.
Ummi A'isha
[3/23, 11:54 AM] Ummi A'isha🏻: [3/23, 11:23
AM] Ummi A'isha🏻: MACE GUDA DAYA TILO.....
ƒ£1⃣

Na
UMMI A'ISHA
Aiki tafara tanayi tana tunanin abin sonta
lamin ita dai Allah ya dora mata sonsa tun ranar
farko data fara ganinsa a makarantar su
shigowarsa taji cikin kitchen din kamshin
turarensa shine ya cika mata hanci tuni taji
jikinta yayi la'asar ta bayanta ya tsaya ya ajiye
kayan yabi bayanta da kallo sannan ya juya ya
fita ajiyar zuciya ta saki sannan taci gaba da
aikinta tana fadin Allah ya kara shirya min kai
lamin, sai data gama dukkan ayyukan sannan ta
nufi dakin sa domin gyarawa tana shiga taga
wata arniya zaune a bakin gadonsa nan da nan
kishi ya motsa saboda duk a tunaninta adakin ta
kwana kallonta tayi tana sanye da wata yar
ficiciyar riga iya cinya kanta taci gashin kanti fal
dubanta tayi tace sannu amma ya zaki zauna
tun safe acikin datti washe baki tayi tace no
zuwana kenan yanzu shima bai san da zuwana
ba nayi mishi surprise visit ne murmushin
takaici tayi ta jawo wani karfe tace yau zan
koya miki hankali jibga mata tayi zata kurma ihu
ta toshe bakinta ta yar da karfen ta soma gaura
mata mari tana cewa waya kawoki wurin mijina?
Yau saina kasheki idanuwan tane suka firfito ita
kuwa marinta taci gaba dayi saida ta kumbura
mata fuska sannan ta kaita waje ta cilla mata
handbag dinta ta dawo taci gaba da gyaran
dakin aranta tana raya cewa har yanxu ina son
mijina kuma zanci gaba da sonsa ya Allah ka
ganar dashi gaskiya tana gama gyaran dakin
yana dawowa alhalin kuma ba haka ya saba
yiba idan ya fice wani lokacin sai dare gabanta
taji yafara faduwa saboda ta tabbata karuwarsa
ce ta fada masa dukan da tayi mata dan haka
cikin sauri ta shige dakinta yana shigowa su
hasna na fitowa falo tambayarsu yayi ina
antynku? Tana daki suka bashi amsa cikin dakin
ya nufa tana zaune bakin gado ki fito ki bani
abinci yunwa nakeji.
MACE GUDA DAYA TILO...
ƒ£2⃣

Na
UMMI A'ISHA
Yunwa nakeji office zan koma ko sai kin bata
min rai? Murna ce ta rufeta tafito ta nufi kitchen
shikuwa mamaki yakeyi wai wannan yarinyar ce
kiri kiri ta hanashi zama a office domin
tunaninta daya addabeshi. Gari na wayewa su
mummy suka dawo dama tayi musu shirye
shiryen karbarsu tayi girke girke da yan soye
soyen karbarsu. Da daddare daddy dakansa ya
shigo bangaren mummy ya kirawo lamin sudai
suna zaune suna sauraron abinda zai faru cikin
fada daddy yafara cewa lamin baka kyauta
mana ba yanzu ashe dama baka da mutunci?
An tabbatar min da cewa kana kawo mata gidan
nan da bama nan cikin sauri junada tace a'a
daddy karya ake yi masa abokan aikinsa ne aka
kawosu basu samu dakiba to shine ya kawo su
nan kafin su samu daki kuma saida ya fada
mana nida su husna cewa zasu zauna kafin a
sama musu masauki sannan kuma daina shiga
dakin yayi har sai da suka tafi cikin mamaki
yabita da kallo su hasna kuwa shiru sukayi
domin sun san wannan maganar ba gaskiya
bace kawai ta fadi hakane danta kareshi amma
ba wani abokan aiki girgiza kai daddy yayi yace
shikenan Allah ya rufa asiri suka amsa da amin
sannan dadyn yatashi ya koma sashensa shima
sashensu ya tashi ya tafi sai faman cika yana
batsewa yake.
MACE GUDA DAYA TILO...
ƒ£3⃣

Na
UMMI A'ISHA
Suna nan zaune a falon mummy, mummy ta
fiddo musu da tsarabarsu ta basu kowa jaka
guda ta ciko masa da kaya, nan suka baje
kayan kowa yana ganin nasa sai murna sukeyi.
Shi kuwa lamin yana can dakinsa yanata
tunanin me junada ke nufi? Anya kuwa yarinyar
nan bata fara sonsa ba? Xumbur ya mike ya
nufi sashen mummy ya taradda su yanda ya
barsu mummy dan Allah baku dawo da maganin
ciwon kai ba? inajin akwai junada ya kalla ki
kawo min ina daki, mummy ce ta shiga dakin da
kanta ta debo mata maganin ta bata, mikewa
tayi ta nufi sashensu ta dauki ruwa a kofi marar
sanyi tana shiga dakin ta sameshi tsaye abinka
ga lecturer ansaba tsaiwa mika masa ruwan tayi
bai karba ba, yace kya iya zubarwa dan ba shine
a gabana ba, agidan uban wa kika zama matata
da zaki rinka korar min yanmata? Ai nafada miki
ni ban daukeki a matsayin mata ba, a yar aiki na
ajiyeki mamakine ya kamata lallai wani mutumin
ba ayi masa gwaninta yaci gaba da cewa banda
ke shasha ce kuma munafuka ina ruwanki da
sha'anina? Cikin bacin rai ta kalleshi gaka nan
babban munafuki mai sabawa Allah da
manxonsa dan nace ni matarka ce shine ina
nufin sonka nake? Allah ya sawwake me zanyi
da mazinaci, kazami mai bin yayan arna? Nayi
hakane dan na kareka daga masifar zina amma
ba don ina sonka ba ko kana nufin ban san illar
shaidar zir ba? Nasani amma nayi don na
tseratar da kai daga fushin iyayenka dan na lura
kana da karancin ilimin addini baka san hukuncin
mazinaci ba taja wani dogon tsaki ta juya tafice
dakinta taje ta kwanta tafara kuka sam bata so
haka ta faruba taso ace yanda ta sauke duk
wani girman kanta take binshi sau da kafa
shima yayi hakuri ya karbeta a matsayin
abokiyar rayuwa kuka takeyi sosai. Shi kuwa
yana nan tsaye inda ta barshi kamar dashen ice
ya kasa koda motsi maganganunta ne kawai ke
masa yawo a kwakwalwarsa abu 3 ne yafi bata
masa rai kalmar data kirashi da ita ta jahili da
kuma kiransa da mazinaci da tayi sannan cewa
me zatayi dashi yafi komai daga masa hankali
da bata masa rai, dakyar ya iya daga kafarsa ya
isa bakin gadonsa ya kwanta kansa sai zugi
yake masa kamar zai rabe gida 2.
[3/23, 11:25 AM] Ummi A'isha🏻: MACE GUDA

DAYA TILO...ƒ£4⃣

Na
UMMI A'ISHA
Kwana 2 yayi yana jinyar maganganunta
kuma tun daga ranar bai Kara yadda sun hadu
ba abinci ma idan ta ajiye masa baya ci yanda
ta ajiye kayanta haka zata dauka bai ko buda ba
abin duniya ya isheta, bayan ta gama ayyukanta
tazo ta tsaya ajikin window ta daga labule lamin
ta hango yana motsa jiki afilin wasa yasa farar
riga irin ta yan ball da wandonta yasa farin
takalmi combos yanata buga kwallo shi kadai
nan ta tsaya tana ta kallonshi har yagama ya
nufo cikin falon labulen ta saki ta nemi wuri ta
zauna a bakin gado su husna ne suka shigo
hasna tace ah anty junada wannan rigar fa?
Hararsu tayi tace ba ason sa ido da sauri husna
tace gaskiya rigar tayi kyau kamar shimi amma
har gwiwa take shigowar lamin ce ta katse
musu maganar yabi junada da kallo ita kuwa da
sauri ta jawo hijab ta saka su hasna ya kalla
yace yaran nan baku da kirki kwana biyu banida
lafiya amma ko ku dubani cikin sauri sukace wlh
yaya bamu sani ba eh amma wadda kuke tareda
ita ai tasani juyawa ga junada sukayi suna cewa
amma anty baki kyauta ba kallo tabishi dashi
yayi kyau sosai yana sanye cikin riga t. Shirt
brown da jeans blue yanata kamshin turaren
Phoenix kallonta yayi yace zakizo ki bani abincin
ko kuwa? Dasauri ta mike ta shiga kitchen ciki
yabita yana tsaye yana kallonta tana zuzzuba
masa abincin har tagama ta dauko zata fito
hanya yabata amma yana tsaye a bakin kofar
tsayawa tayi tace zan wuce to ki wuce mana ko
na hanaki ne? Ahaka ta wuce amma dole saida
ta dan bugeshi sannan ta iya wucewa bayanta
yabi har suka isa dining area din.
[3/23, 11:40 AM] Ummi A'isha🏻: MACE GUDA

DAYA TIILO..ƒ£5⃣

Na
UMMI A'ISHA
Kallo ya ringa binta dashi har ta gama
zuzzuba masa ta ajiye masa ta wuce dakinta
murmushi yayi yafara ci. Wasa wasa sai jinsa
yayi ya wayi gari da matsanancin son junada
kuma tun ranar data gaggaya masa
maganganun nan yaji zina ta fita daga ransa
baya sha'awar aikatata dan haka tuni yafara
neman gafarar ubangiji ba dare ba rana. Gaba
daya sonta yagama shigarsa ta ko ina bashi da
buri illa kasancewa da ita dan haka ya daura
aniyar nuna mata so afili tare da bin duk wata
hanya domin yasamu ta shaku dashi, yau sai 5
yadawo domin meeting sukayi kansa tsaye ya
wuce side dinsu amma ya tarar bata nan ya
tabbata tana wurin mummy dan haka ya nufi
can din yana shiga ya tarar da mummy a
babban falo tana waya ita kuma dama yaji
motsinta a kitchen dan haka kitchen din ya bita
ya taradda ita tana fere doya kamshin turarensa
kawai taji tasan yashigo tsayawa tayi cak daga
aikin da take bayanta ya karaso yazo ya tsaya
ahankali tamkar mai yin rada yace wai ni
meyasa duk abinda kikeyi daga kin ganni sai ki
daina sai kace wani dodo? Saboda ina sonka
tafada acikin zuciyarta amma a fili shiru tayi
bata amsa masa ba, da rana me kuka dafa?
Tuwon shinkafa ta bashi amsa yanzu kuma me
zaki dafa? Soyayyiyar doya da miyar koda
murmushi yayi to ni yanzu me zaki bani? Dan
yunwa nakeji babu abinci amma akwai snacks
to kawo min snacks din da juice tana jiyowa
sukaci karo sorry ya fada tareda ja baya ya
koma falo murmushi junada tayi tace Allah
yakara shirya min kai lamin yana zuwa ya zauna
kusa da mummy hayaniyar su husna ya ji a
dayan falon ya kalli mummy me yaran nan
sukeyi ne? Kallo mana mummy ta bashi amsa
murya ya daga hasna kuzo nan suna zuwa ya
fara masifa wato ku baku da aiki sai kallo ko?
Kun bar junada ita Kadai da aiki kuna jira ta
gama ta kawo muku kuci ko saboda ga baiwa?
To wlh baku isaba kune zaku rinka girki ba
matata ba ku tashi ku shiga kitchen ku karasa
aikin da takeyi tashi mummy tayi tana fadin
dakyau ka kyauta yara yan mata dasu amma ba
su iya girki ba idan akayi aurensu ya zasu yi ta
shigewarta dakinta su kuma su hasna suka
shiga kitchen juyowa yayi ga junada wadda tun
dazu take rike da kaya a hannu tana jiran ya
karba.
MACE GUDA DAYA TILO..
ƒ£6⃣

Na
UMMI A'ISHA
Mika masa tayi ya karba yana cewa kar ki
kara yi musu girki a marerece tace ai basu iya
ba kallonta ya sakeyi yace karya suke sun iya ki
rabu dasu dolensu suyi falon taga yayi gaje gaje
kamar ba agyara ba dan haka tsayawa tayi
tafara gyara falon ahankali yafara binta da kallo
wannan yarinyar gaskiya kyakkyawa ce ta ajin
karshe sai wanda yake kusa da ita ne ma zaifi
tabbatar da hakan ta hadu ta ko ina da haka
yagama cin snacks din yatashi ya fice ya nufi
side dinsu ita kuwa dama duk a takure take
yana fita ta tashi ta shiga kitchen wurinsu
husna. Sai dare tabar side din mummy tare dasu
hasna domin har yanzu basu dawo sashen
mummy ba sanda suka shiga yana falo yana
kallo sannu yaya su hasna suka fada suka shige
kai kuzo nan ya fada jiyowa sukayi suka dawo
junada ya kalla wannan yaran har yanzu anan
suke kwana? Kai ta daga masa tace eh kallonsu
yayi to wlh kun kusa komawa inda kuka fito
dalla ku wuce ku bawa mutane waje da sauri
suka wuce ya kalli junada kawo min ruwan zafi
amma empty kar kisa milk to ta amsa masa ta
shiga cikin kitchen ta hado masa ta kawo masa
rissinawa tayi ta mika masa karba yayi yana
kallon yan yatsunta wanda suke tsananin
burgeshi tana bashi ta wuce dakinta. Washe gari
da wuri ta tashi ta gama abubuwan da za tayi
ta shirya domin ranar zasu fara exam tun 8:30
suka tafi lokacin ko tashi daga bacci baiyi ba
lokacin data shiga dakinsa kwance ta ganshi
daga shi sai gajeren wando ko riga babu
ajikinsa,ya kure A. C baccinsa yake hankali
kwance, kallonsa ta tsaya ta farayi fatarsa sai
sheki take kamar ta mace da gani zatayi laushi
ko ina najikinsa gashi ne ya kwanta luf luf wani
irin kyau taga yayi mata sleeping beauty ta fada
ahankali ta fice daga dakin. Shi kuwa lokacin da
ya tashi ya shirya ya fito sai yaji falon tsit da
alama sammako sukayi zuwa makaranta.
Ummi A'isha🏻
[3/23, 11:54 AM] Ummi A'isha🏻: [3/23, 11:45
AM] Ummi A'isha🏻: MACE GUDA DAYA TILO

....ƒ£7⃣

Na
UMMI A'ISHA
Falon ya fito yakarasa kan dining yaga flasks
a jere, yafara budewa soyayyen dankali da kwai
yaga sai kamshi yake, ya bude dayan farfesun
kaji ne shima kamshine kawai ke tashi duk
abinda tasan yana bukata ta hada masa nan ya
zauna ya cika tumbinsa sannan ya nufi cikin
dakinta yana shiga yaji kamshin room freshener
dana turaren wuta sun hadu sun doki hancinsa
dakin nata yafara kallo komai tsaf tsaf babu
datti ko daya gefen gadonta yaje ya kwanta
aransa yana tunanin cewa ya kamata ya ajiye
duk wani girman kansa ya rungumi matarsa ya
nuna mata soyayya dan tabbas yar halak ce duk
matsayinta da mukamin mahaifinta amma ta
kaskantar da kanta take yi masa bauta har
kayansa ta ke wankewa ga wulakancin datake
fuskanta daga wurinshi amma duk ta jure wani
irin juyi yayi akan gadon yace nayi alkawari sai
nayiwa junada abinda zata soni, zata kaunace ni
tashi yayi yakoma dakinsa domin duk ba yajin
dadin jikinsa sakamakon rashin ganin junada
dan haka yau bazashi aiki ba. Yana nan kwance
ya saka fari ya saka baki har ya kwashe awanni
bai ankara ba ya jiyo hayaniyarsu acikin dakin
junada, tashi yayi ya nufi dakin nata lokacin
hasna tana daya dakin tana wanka ita kuma
husna tana tsaye tana sanye da wata doguwar
shimi ta bawa kofar shigowa baya tana shirya
lecture note dinta ita kuma junada dogon wando
ne ajikinta da bra tana zaune akan gado tana
facing din kofa ta sunkuyar da kanta tana duba
questions paper din su husna gaba daya
hankalinta yana kan question paper din yana
shiga ya ganta yasalam ya fada sadaf sadaf ya
juya da niyyar ficewa amma sai aka samu akasi
kafarsa ta bugi kofa dago kanta tayi tana
dagowa suka hada ido wata kunya ce ta
lullubeta shi kuwa cewa yayi sorry you are
changing? Ya fice daga dakin hankalinsa a tashe
acikin ransa yana cewa lallai ashe yarinyar nan
lullube take da baiwa iri iri shiyasa take yanga?
Lallai da yaso tafka babban kuskure a
rayuwarsa, ita kuwa junada haka kawai ta kasa
jin zafinsa amma taji wata azababbiyar
kunyarsa ta kamata.
MACE GUDA DAYA TILO...
ƒ£8⃣

Na
UMMI A'ISHA
Tun daga lokacin ta daina yarda su hadu,
wasan buya suka shiga tun bai gane ba har
yagano kunyarsa take ji murmushi kawai yayi
yace yaro yaro ne. Ahaka ahaka har suka kusa
gama exam dama shi kawai kyaleta yayi tagama
exam din lokacinne zai fito mata da manufarsa a
fili, da daddare yashigo a babban falo ya iskesu
suna cin abinci suna kallon wani Nigerian film
mai suna i promise kowa rike da filet dinta a
hannu gaba daya hankalinsu ya tattara akan
film din ahankali yazo kusa da junada ya zauna
batare da sunji motsin sa ba magana yayi yace
sannunku sarakan kallo gaba dayansu babu
wadda bata tsorata ba dan sam basuji shigowar
sa ba kallo junada ta fara binsa dashi yayi kyau
sosai rigar jikinsa maroon colour an zana
tsintsaye guda uku ajiki an rubuta Angry Birds
brown din jeans yasa kamshin turaren sa kamar
kullum ya baibaye wurin,husna ce tayi dariya
tace gaskiya yaya ka bamu tsoro wlh junada ya
kalla wadda har yanzu itama shi din take kallo
murmushi yayi yace ga babbar matsoraciya nan
wadda take neman cinye ni da ido dariya suka
sa ita kuwa murmushi tayi ta dauke kanta daga
kallonsa abincin nata ya dauka yace matso muci
nima yunwa nake ji kallonsa tayi tace ni na
koshi kaci sai in karo maka tsareta yayi da ido
tamkar mai yin rada yace wlh baki isa ba sai
munci abincin nan tare kafada ta make ahankali
ahankali yafara matsowa har yazo kusa da ita
sosai ya kamo hannunta daga shi har ita wani
bakon al'amari ne ya ziyarce su wani irin yarr
taji ajikinta, su husna kuwa tsayawa sukayi suna
ganin ikon Allah, ganin bazata ci ba yasashi
kwanto da ita jikinsa ya debo yana shirin bata
tamkar wata jaririya kunya ce ta kamata ganin
su hasna na kallonsu shi kuwa yama manta
dasu na wurin ganin taki ci yasa yajiyo asannan
ne ya gansu korarsu yayi yace kai ku bar nan da
sauri suka mike suka shige daki suna shigewa
ya jiyo gareta yasa tattausan hannunsa ya
kamo hannunta wanda ya dade yana burgeshi
ahankali yafara murza yan yatsunta acikin
hannunsa wani irin taushi da laushi yaji a
hannun nata tuni ya shagala yama manta da
batun abinci.
[3/23, 11:50 AM] Ummi A'isha🏻: MACE GUDA

DAYA TILO...ƒ£9⃣

Na
UMMI A'ISHA
Ahankali ta zare hannun nata daga cikin
nasa ta kalleshi tace to kaci abincin kace yunwa
kakeji kallonta shima yayi idanuwan shi sun
canza launi yace ai nace miki tare zamuci tashi
tayi taje cikin kitchen ta zubo abincin ta dawo
wurin shi ta ajiye akan stool din gabansa
kallonta yayi yace to muci kinga cokalin guda
daya ne don haka sai muyi kama kama zama
tayi a kusa dashi abincin ya fara ci ya miko
mata cokalin karba tayi itama tafara diba tana
ci shi kuwa gaba daya hankalinsa yana wajenta
ahaka har suka gama cin abincin mikewa tayi
da nufin zuwa ta dauko musu ruwa da sauri ya
kamo hannunta yace barshi na dauko mana a'a
ka barshi zan dauko no barshi kawai mikewa
yayi yaje fridge ya dauko musu ruwan da kofi ya
dawo wajenta yace zakisha da kanki ko na baki
a baki? A'a zan sha da kaina tsiyayo mata yayi
ya mika mata ta karba tasha sannan ta mika
masa shima yasha, mikewa tayi tace zan shiga
daki binta yayi yace to muje tana gaba yana
biye da ita har cikin dakin a gefen gadonta ya
xauna ita ma zaman tayi domin a takure take
gashi tana son tayi wanka amma bazata iya
tashi tashiga a gabansa ba.
MACE GUDA DAYA TILO...
ƒ£0⃣

Na
UMMI A'ISHA
Tashi yayi yace to sai anjima Allah ya jima
damu tafada a hankali fita yayi daga cikin dakin
ya nufi dakinsa ita kuma wanka ta tashi ta
shiga tana fitowa ta ganshi tsaye daga shi sai
gajeren wando da farar best kallonta yafara yi
sosai daga ita sai dan guntun towel, gashin
kanta har kugunta sai faman kamshin mai dadi
takeyi na sabulun da tayi wanka dashi yaya
lamin me kake so? Ta fada cikin rawar murya
kamar wanda yake koyon magana yace ruwan
wanka zaki zo ki hada min to ina zuwa ta bashi
amsa acikin zuciyarta kuwa cewa take aikin
nawa ya karu kenan tunda yanzu har dasu zuba
ruwan wanka, tsaye ya tsaya mata yaki fita
jiyowa tayi tace ina zuwa shiryawa zanyi
kallonta yayi sannan yace to shirya mana ko na
hanaki ne? Ganin bashida niyyar fita yasa ta
tattaro gashin kanta ta tufke tamkar gammo a
kunyace ta dauki dogon hijab ta sa tazo zata
wuce jawota yayi yace tsaya mana madam kisa
kayanki mana a'a sai na dawo zan sa to
shikenan muje wucewa tayi izuwa dakin nasa ta
shiga bathroom ta hada masa ruwan wanka
harda turaren wanka ta zuba masa ta fito
lokacin yana waya sunan Jen taji ya ambata
dan haka ba tayi wata wata ba ta fice daga
dakin cikin sauri zuciyarta sai faman tafarfasa
takeyi wato arnan nan ba zasu kyale mata lamin
ba ko? Allah yasa yarinya tayi gangancin zuwa
mata gida wlh sai ta raunata ta da wannan
tunanin ta shitya cikin rigar baccin ta ja mai
kyan gaske ta jawo hand out dinta ta soma
karantawa domin tana da exam gobe dama guda
2 ne suka rage mata. Washe gari ta tashi ta
hada breakfast ita dasu husna dankali da kwai
ta soya musu shi kuma lamin plantain da kwai
ta soya masa tayi masa farfesun kayan ciki ta
zuba masa ruwan zafi a cikin flask tazo ta jera
akan dining ta nufi dakin su husna taje ta taso
su agurguje suka shirya suka fito amma sai da
junada ta leka dakin lamin inda yake kwance
yanata shakar baccinsa da sauri taja masa
kofar ta fita cikin sauri suka shiga sashen
mummy suka gaidata sannan suka wuce
makaranta.
Ummi A'isha🏻
[3/24, 12:34 PM] Ummi A'isha🏻: [3/24, 10:11
AM] Ummi A'isha🏻: MACE GUDA DAYA TILO..
ƒ£1⃣

Na
UMMI A'ISHA
Karfe 9 ya tashi yayi wanka yafito cikin
bakaken suit wanda sukayi masa kyau sosai,
kan dining yaje ya xauna yayi break yana
gamawa ya shiga dakin junada yauma kamar
kullum dakin a tsaftace yake sai kamshi ne yake
tashi fitowa yayi ya nufi side din mummy ya
gaisheta sannan yatafi office. Yau tun 1 suka
fito daga paper da wuri suka dawo gida su
hasna daki suka shige suna ramuwar bacci ita
kuwa junada kitchen ta fada tafara kacaniyar
hada abincin rana inji turawa sukace lunch, faten
doya da danyen kifi tayi tana gamawa tashiga
wanka yauma tana fitowa ta ganshi a tsaye
kamar jiya sannu da zuwa tace dashi yawwa
sannu ya amsa mata ganin kallon da yake mata
yasa tayi saurin sunkuyar da kanta kizo kibani
abinci amma bari nima naje nayi wanka kafin ki
gama shiryawa ya juya yafita, agurguje ta shirya
cikin wani bakin lace mai digon pink ajiki anyi
masa zanen fulawa ajiki dinkin riga fitet da skirt,
turaren urban woman shine turarenta ta feshe
jikinta ta nufi falo tana fitowa shima yana fitowa
yayi wanka ya canza shiga cikin wata riga
purple colour anyi zanen heart kanana an rubuta
cute style a tsakiya da wando brown, gayen nan
akwai iya daukar wanka tafada acikin zuciyarta
kujera yaja ya zauna ta zuba masa abincin ta
koma falon ta zauna tana hango shi yana cin
abincin shi kuwa mamaki yakeyi wai duk lokacin
da yarinyar nan take kusa dashi sai ya tsinci
kansa cikin farin ciki amma da zarar bata nan
sai ya samu kansa cikin tashin hankali tab!
Allah mai yadda yaso.
MACE GUDA DAYA TILO...
ƒ£2⃣

Na
UMMI A'ISHA
Ahankali ahankali yake cin abincin har ya
gama, wayoyinsa ya tattara yataso daga dining
area din cike da ladabi tace yaya lamin dama
ina son yin magana dakai, kujerar dake kusa da
ita yazo ya zauna yace ina sauraronki dama dan
Allah idan nagama exam ina so kabarni naje
bauchi kallonta yayi yace me akeyi? Babu
abinda akeyi ta fada tana wasa da yan yatsun
hannunta wani hamshakin murmushi yayi
sannan yace to idan kin tafi ni kuma ki barni
dawa? Kiyi hakuri zakije bauchi amma ba yanzu
ba kinji? Kai ta daga tace to shikenan a falon
tabarshi ta shiga dakinta, yana nan zaune har
su hasna suka fito harara yafara aika musu da
ita sannan yace wato baku ji abinda nace muku
ba ko? Allah yabaku sa'a tashi yayi ya nufi side
din mummy. Washe gari suka gama exam sun
samu hutu harna 3 weeks dan haka yanzu sai
zaman gida babu inda suke fita shima lamin
hutun sukeyi dan haka kullum yana gida, gaba
daya ya canza ya daina shan kunu da babbata
rai yana bin duk wata hanya da zasu shaku da
junada kuma yana kokarin kyautata mata a
kowanne lokaci,yauma tana kitchen tana girka
abincin dare yashigo su husna kadai yaga a falo
suna aikin kallon wani American film mai suna
prison break ko magana baiyi musu ba ya wuce
kitchen din lokacin daya shiga tana tuka tuwon
semo vita ahankali ya lallaba ya rufe mata ido
tana jin hannunsa tasan shine domin komai
nasa kamshi yake na turarensa, murmushi tayi
tace yaya lamin murmushi shima yayi yadawo
kusa da ita yace sannu da kokari yawwa sannu
da zuwa tafada tana kwashe tuwon kawo na
kwashe miki yafada yana kallon fuskarta a'a ai
baka iya ba tafada waya gaya miki? Ki tambayi
mummy kiji idan ban iya ba a'a ni basai na
tambayi mummy ba su hasna zan tambaya to ai
lokacin da nakeyi su husna basu da wayo a'a to
duk yadda akayi baka iya ba na iya mana ko
lokacin da nake Malaysia nine nake girki na ba
girki kakeyi ba take away kake ci ai nasani a'afa
kar kisa nayi fushi gobe kina tashi kiga nagama
shirya breakfast hmmm da kuwa kaga nafi yarda
da abinda ka fada uhm kinga zaki sa yau naki
yin marking din papers din dalibai na tunda kince
ban iya tuwo ba a'a wasa nake ka iya tuwo
harda miya daidai lokacin tagama kwashe tuwon
taje ta sauke miyar danyar kubewar data yi ta
kalleshi to idan bakayi wa dalibanka marking ba
yaya zakayi dasu? Kowa yasamu carry over
yafada yana ficewa daga cikin kitchen din.
[3/24, 10:21 AM] Ummi A'isha🏻: MACE GUDA

DAYA TILO..
Na
UMMI A'ISHA
ƒ£3⃣

Bayanshi tabi da kallo tana murmushi saida
tagama shirya komai acikin flask sannan ta
debo ta kawo kan dining ta jajjera ta karasa
wajen su husna wanda suke zaune sun kurawa
tv ido suna kallo, gefensu taje ta zauna itama ta
fara kallon, lamin ne ya fito shima yazo gefenta
ya zauna daga shi sai short nicker da farar riga
body hug laptop dinsa ya ajiye akan Stoll din
dake gabansa ya miko mata wata takarda ungo
rinka fado min mark din ko wanne dalibi karba
tayi tafara karanto masa kallonsa tayi yanzu fa
muma da dalibanka ne tsaf zaka bamu carry
over ko? Kwarai kuwa shi yafi komai sauki ma
musamman ma wadannan yaran masu masifar
kallon tsiya murmushi tayi ta kalleshi ya
sunkuya ya dukufa yana daddana laptop din
fuskarsa dauke da murmushi fado min mark din
Khadija Aminu 25 a'a ban yarda dakeba sai dai
35 don yarinyar tanada kokari kusanma tafi duk
matan ajin kokari ras taji gabanta yafadi to ko
itama budurwarsa ce? Tafada acikin ranta kin
san ku mata baku fiya karatu ba shiru tayi masa
bata bashi amsa ba shi kuwa bai ma san Kalmar
daya fada ya bata mata rai ba da haka suka
gama fuskarta babu walwala shima saiya samu
kansa cikin damuwa, kiran sallar magribar da
suka jiyo ana kwallawa a masallacin gidan ne
yasasu tashi gaba dayansu,nan yabar kayan
aikin nasa yashiga dakin junada a bathroom
dinta yayi alwala sannan yafito ya tafi
masallaci, abinda yake Kara burge junada kenan
domin sam lamin baya wasa da sallah, yana
fitowa daga masallaci sashen daddy yawuce
anan ya taradda mummy murmushi yayi yace
mummy kema nan kika taho? Dariya tayi tace to
ai babana kune kuka kwashe min abokan hirar
tawa sai asannan daddy yayi magana yace to
shi basai yana zuwa yana tayaki hirar ba zama
yayi akusa da daddy yace to ai sai nazo indai
mummy tace nazo din, ko cewa tayi nadawo
gaba daya ma sai nadawo dariya sukayi gaba
dayansu daddy yace ina matar taka take?
Kwana 2 ban ganta ba amma ina ganin girkinta
kullum murmushi mummy tayi tace ai gaskiya
yayi dacen mata yarinyar nan karfi da yaji ta
hanani yin girki kullum sai dai ta dafa ta kawo
min ta dauke ni tamkar mahaifiyarta Allah yayi
mata albarka shidai lamin shiru yayi amma har
cikin ransa yaji dadyn yabon junada dasu daddy
sukayi dama yasan dole su mummy su sota
domin ko acikin yayansu sunfi sonshi,son da
suke yi masa nema ya shafi matarshi.
MACE GUDA DAYA TILO..
Na
UMMI A'ISHA
ƒ£4⃣

Anan ya zauna har saida aka kira sallar isha
sannan suka tafi masallaci shida daddy, yana
fitowa daga masallaci ya wuce side dinsu nan
ya taradda su sun baje suna cin tuwo gaban
junada ya je yasa hannu acikin kwanonta yafara
cin tuwon sudai su husna mamakin yayan nasu
sukeyi kwana biyu domin duk ya canza sai
tattalin matarsa yake gamida tarairayarta
murmushi yayi mata yace gaskiya miyar nan
tayi dadi itama murmushin tayi tace ko? Eh
mana ai tayi dadin da bazai misaltu ba gobe ma
kiyi mana ita kin san ita kubewa tanada
mutukar amfani ajikin dan adam likitoci sun
tabbatar da haka dariya tayi tace to kai kuma
yaushe kabar lecturing ka koma doctor? Ranar
da kika bar daliba kika koma noman kubewa
dariya tayi masa sosai sannan tace gaskiya ya
kamata nasa maka waigi dan naga alama santi
kake murmushi yayi ai tuwon naki ya kai
matsayin da za ayi masa santin yanzu daddy
ma nasan yana can yana santin wannan miyar
kubewar hmmm kai dai tunda kayi shikenan
yana koshi ya mike idan kin gama ki shigo min
da laptop dina da sauran kayan cikin daki to ta
amsa masa dakinsa ya wuce yaje ya kunna
labarai a BBC yana kallo sai wurin 9 sannan
tashiga dakin nasa da laptop din a hannunta ya
baje akan gado yana kallo daga shi sai gajeren
wando idonta ta sauke kasa batare data kalleshi
ba tace ga kayan naka ajiye anan kishiga
bathroom ki hada min ruwan wanka, wanka
zanyi ajiyewa tayi ta shiga cikin bathroom din
sai data dan wakeshi tafesa air freshener mai
kamshi sannan ta hada masa ruwan wankan ta
fito na zuba maka to ki jirani na fito sai mu
karasa wannan aikin ko? Tom ta nemi wuri ta
zauna agefen gadon bai dade sosai ba yafito ya
sameta zaune inda ya barta.
MACE GUDA DAYA TILO...
Na
UMMI A'ISHA
ƒ£5⃣

Bakin gadon shima yaje ya zauna ya kamo
hannunta ya rike cikin nasa junada ita dai shiru
tayi tana ganin ikon Allah murmushi yayi ya dan
kalleta yace junada kalleni kin kallonsa tayi
magana ya sakeyi ki kalleni junada ni mijinki ne
abokin rayuwarki, komai da kikaga yana da
sanadi kuma akwai yadda yake zuwa yanzu ki
tashi kishiga toilet ki dauro alwala kizo mu
gabatar da sallar ma'aurata tunda kin korar
mun yan mata kinga sai ke ki dauki dawainiya
ta dam! Taji gabanta ya fadi me lamin yake nufi
ta tambayi kanta dubansa tayi cike da mamaki
ta fizge hannunta daya rike cikin nasa tace
ma'aurata? A ina na zama matarka? Ta ina
muka zama ma'aurata? Kamanta abubuwan
daka fada a baya? Kai da bakinka kace ba ka
daukeni a matsayin mata ba a yar aiki ka
ajiyeni, dan haka ina son kabarni a matsayin yar
aikin kamar yadda zuciyar ka ta kudurta tun
farko kar ka canza min matsayi daga yar aiki
kuma yanzu duk abinda zaka fada bazai yi tasiri
agareni ba saboda nasan ba gaskiya bane
kafada ne kawai saboda ka cimma wata manufa
taka tana kaiwa nan ta tashi fuuuuu! Tafice ta
bar dakin shi kuwa lamin yakasa koda motsi
dama yasan dole sai haka ta faru tsakaninsu
duba da yadda haduwarsu ta kasance tun
farko,wani guntun tsaki yaja to ita wannan
yarinyar me takeso tace? Nufinta ba sonta yake
yiba kawai sha'awarta yake? Mts dama haka ita
zatayi tunani gani zatayi kamar sha'awarta nake
dan haka da zarar na cika burina zan daina
kulata alhalin kuma ba haka bane alokacinne ma
zanfi kulawa da ita zanfi nuna mata tsantsar
soyayyar da nake yimata, zan nuna mata kauna
wacce bata samu ba afarkon aurenmu yafada
acikin zuciyarsa.
UmmiA'ishah
[3/24, 12:34 PM] Ummi A'isha🏻: [3/24, 10:28
AM] Ummi A'isha🏻: MACE GUDA DAYA TILO...

Na
UMMI A'ISHA
ƒ£6⃣

Ji yayi zuciyarsa ta fara tafarfasa kamar ana
hada mata wuta lallai ma yarinyar nan to itada
ahaka zasuyita zama? Wannan ma ai shirme ne
kuma ba mai yuyuwa bane tunda shi yanada
bukata ita kuma ta tsare ta kasa ta hanashi
kula ko wacce mace sai ita kadai MACE GUDA
DAYA TILO tashi yayi yafara zagaye dakin nasa
yayinda bacci kuma yayiwa idanuwansa kaura.
Ita kuwa junada tana zuwa daki tafara godewa
Allah domin ta san yafara amsar add'arta tunda
gashi har lamin yafara nuna son kasancewa da
ita ina sonka lamin tafada acikin zuciyarta wani
murmushi tayi sannan tace zan mallaka maka
kaina amma ba yanzu ba sai lokacin dana
tabbatar da ka gama kamuwa da ciwon sona
kagama yarda da cewa nikadai ce MACE GUDA
DAYA TILO acikin zuciyarka da wannan tunanin
ta tashi tayi shirin bacci tayi kwanciyarta ba
tare da damuwar komai ba shi kuwa lamin yana
can yana ta faman sintiri atsakar dakinsa kamar
wani soja awannan daren dai sai bacci barawo
shine yayi nasarar sace shi daf da asuba. Da
misalin 8 ta fito ta shiga kitchen kamar kullum
ta shirya lafiyayyen breakfast ta kawo kan dining
ta jera tana gamawa ta shiga dakinta tayi
wanka ta fito tashirya cikin wata body hug baka
mai dan siririn hannu da wata bakar skirt ta
matseta sosai ta gyara gashin kanta ya sauko
har gadon bayanta ta feshe jikinta da turaren
urban woman tasa wata bakar hula mai gashi ta
nufi falo tana fitowa ta hangoshi akan dining a
zaune ya zubawa abincin ido fuskar nan tasa
tayi mutukar kyau yana sanye da orange colour
din t. Shirt mai gajeren hannu da blue din jeans
hannunsa daure da agogo golden colour gaba
daya falon ya gauraye da kamshin turarensa
manyan idanuwansa ya dago yafara kallonta
fuskarta tasha make-up kayan da tasa sunyi
bala'in matseta kuma sunyi mata kyau abunka
da farar mace nan da nan yaji ya rude ya nemi
nutsuwarsa ya rasa tuni hankalinsa ya soma
neman tashi kallo kawai yake binta dashi dakyar
ya iya furta pls zo ki hada min tea din,
ayangance kamar mai tausayin kasa ta tako
zuwa kan dining din ta dan russuna yaya ina
kwana acan kasan makoshinsa yace lfy beauty
MACE GUDA DAYA TILO
Na
UMMI A'ISHA
ƒ£7⃣

Tea din ta fara hada masa sai wani shan
kamshi take shi kuwa lamin yasaki baki sai
binta da kallo yake sai kace wani soko tana
gama hadawa ta kawo gabansa ta dire masa ta
juya zata tafi hannunta taji ya ruko cikin nashi
jawota yayi ya zaunar da ita akan cinyarshi
yafara murza yan yatsunta cikin nashi ahankali
kamar kullum yarr! Taji nan da nan ta tuno da
yan matansa acikin zuciyarta tace yanzu suma
haka yake yi musu ko? Wata zuciyar tace mata
fin haka ma yayi kamar wadda aka tsikara tayi
zumbur ta mike ta fincike hannunta kallon
mamaki yabita dashi wai junada meye yake
damunki ne?. Bata kalleshi ba ta wuce daga
dining area din falo taje ta zauna ta kunna kallo
tana nan zaune har ya gama yin break din ya
taso ya dawo falon ya zauna yana zama ta
tashi ta shige dakinta tayi zamanta abin duniya
ya taru yayi masa yawa shima mikewar yayi ya
nufi side din daddy anan ya iske mummy zama
yayi suka fara hira babu laifi ya dan jin saukin
damuwar da yake ciki. Anan ya kusan wuni sai
da yamma yakoma side dinsu yana shiga ya
tarar dasu husna suna zaune a falo ita kuma
junada yajiyo motsinta a kitchen dakinsa
yashiga yayi wanka yafito cikin ash colour din
riga da bakin wando kansa tsaye ya shiga
kitchen hangota yayi tana kaiwa da kawowa
acikin kitchen din daga ita sai wata yar
mitsitsiyar shimi ja da dogon wando masha
Allah yafada acikin zuciyarsa ahankali ya karasa
daf da ita ya tsaya tana jinsa taki jiyowa ta
shareshi gyaran murya yayi sannan yace sannu
da aiki beauty sunan taji har cikin ranta ita dai
tana son muryarsa shiyasa take son taji yana
mata magana koda kuwa fada ne jikinta ya
matso ya ziro hannuwansa ta bayanta yace
kawo in yanka miki salak din a'a kabarshi
nagode ta fada cikin wata iriyar murya domin
gaba daya ya gama rikitata lokaci daya saboda
duk yabi ya dabaibaye ta ya hanata sakat kafa
sakar min nauyinka nauyi kuma? Ni wanne nauyi
gareni? Au kai bakasan kanada nauyi ba? Ni
banida wani nauyi babu mamaki ma idan akace
kin fini nauyi uhm anya kuwa zan fika nauyi? To
ko za agwada ne? A'a ba sai mun gwada ba
tafada tana girgiza kai hmmm yayi murmushi ke
kin fiya raki dayawa.
MACE GUDA DAYA TILO
Na
UMMI A'ISHA
ƒ£8⃣

Kin fiya raki da yawa tun yanzu kin fara
cewa inada nauyi anya kuwa zaki iya naukar
nauyina? A'a bazan iyaba tayi masa gatse acikin
zuciyarta kuwa cewa take wadan nan tsiga tsiga
matan ma suka iya daukar ka balle ni?
Hannuwan shi ya janye daga jikinta yace natafi
masallaci ya juya yafita ita kuwa wata ajiyar
zuciya ta sauke. Tunda ya fita salla bai dawo ba
sai bayan sallar isha yau falon babu kowa
mamaki ne ya kamashi to ina suka shiga?
Dakinta ya nufa ya murda yajishi a kulle yadawo
nasu hasna shi kuma a bude yake amma basa
ciki duk yadda akayi suna side din mummy
yafada acikin zuciyarsa can din ya nufa
yasamesu sunata hira da mummy amma babu
junada ganin haka yasa ko zama baiyi ba yafice
sai yanzu ya gano wato daki ta shiga ta rufe
kenan dan kar ya bukaci wani abu agurinta tsaki
yaja yace ni kuwa zan baki mamaki junada in
dai nacika lamin baxan sake nuna miki bukatata
akanki ba kan dining yaje ya samu ta shirya
komai faten dankali da hanta sai salad data
hada masa domin tasan shi yana son salad
zama yayi yaci ya koshi sannan ya shiga
dakinsa wanka yayi abin mamaki hatta ruwan
wankan ta hada masa murmushin mugunta yayi
yace yarinya ina tausaya miki cike da damuwa
yayi baccin wannan rana.
[3/24, 10:32 AM] Ummi A'isha🏻: MACE GUDA

DAYA TILO
Na
UMMI A'ISHA
ƒ£9⃣

Washe gari da safe ya tashi yayi wanka ya
shirya ya fito yauma kamar jiya taci ado tamkar
baturiya cikin wata doguwar Riga dark brown
shara shara mai hannun shimi ta tufke gashin
kanta wanda yake lodi guda ta kame akan kujera
har cikin zuciyarsa yaji sonta ya ratsashi babu
karya ta tafi da imaninsa ahankali ya jefeta da
wani irin kallo wanda shi kadai yasan
ma'anarsa falon yashiga ya zauna ina kwana
yaya lamin tace dashi cike da murmushin da
yake karawa fuskarsa kyau yace lfy lau kawo
min tea kawai yau babu abinda nake sha'awar
ci kallonsa tayi nayi maka farfesu fa a'a ki ajiye
min anjima zanci yanzu fita zanyi tashi tayi taje
ta hado masa ruwan zafin ta kawo masa kadan
yasha sama sama yatashi ya kwashi wayoyinsa
da key din motarsa ya fita lekensa ta farayi ta
window ga mamakinta sai taga ko side din
mummy bai kalla ba ya shiga motarsa yafita
daga gidan to ina ya tafi?? Ta tambayi kanta
karfa yakoma yawon bin matan da yasaba
gabanta taji ya fadi ya Allah ka kare wannan
bawa naka,ka kawar da idonsa daga kan matan
banza Allah ka dawo min dashi lfy wani irin
kishine taji yana taso mata agaskiya tana kishin
lamin sosai domin tasan mijinta ya hadu ta
kowanne bangare tamkar tauraro yake acikin
taurari kana ganinsa kaga cikakken bafulatani
yanayin da taganshi lokacin da yana bacci ne ya
fado mata hmmm dole yan mata suna rububinsa
domin kyansa ya isa.
MACE GUDA DAYA TILO
Na
UMMI A'ISHA
ƒ£0⃣

Haka ta zauna sukuku ko tea dinma ita
takasa sha domin duk a tunaninta yawon neman
mata ya tafi musamman ma yau da taga ko
sha'awar taba hannunta bai yi ba, nan ta nemi
wuri ta zauna tanata sakar zuci ta na nan zaune
har su husna suka tashi daga barci suka fito
sukazo suka isketa a falon suka fara kokarin yin
break ita kuwa hirar da suke yimata sama sama
take ji domin bata cikin nutsuwa hankalinta
naga abin sonta lamin ni dai ummi A'isha yar
kallo ce, tana nan zaune motsi kadan ta kalli
agogo har 12 tayi ganin bai shigo ba yasa ta
tashi tashiga kitchen tabar su husna suna kallon
wani Indian film atashar zee aflam mai suna
muhabbatien,aiki take amma sam babu walwala
da sukuni a tattare da ita ahaka ta gama hada
hadaddiyar fried rice dinta wadda tasha hanta
da carrots ga cabbage yaji sai kamshi take tayi
wara wara da ita gwanin sha'awa dan ko ni
ummi A'isha saida naji yawuna ya tsinke, tana
gama hada fried rice din ta soya naman zabbi
tayi masa kykkyawar suya ta tattara komai ta
zuzzuba a cikin food flask ta kawo kan dining
tafara jajjerawa su husna dake falo suka fara
tandar baki hasna ta taso tace Anty me kika
girka mana ne? Hararta tayi tace mijina nayiwa
girki ku jira idan yaci ya rage sai ku karashe
sauran dariya hasna tayi ta koma falon tana
fadin to bari mu zauna zaman jiransa husna
dake zaune tana sauraronsu tace ai kema hasna
nasha fada miki mu tattara mu koma sashen
mummy amma kika ki gashi nan ai muna ganin
wariyar launin fata awajensu dariya sukayi
hasna tace ai Anty tana shagwaba yaya tafi
sonsa ma akanmu murmushi junada tayi tace ai
dole dama nafi sonsa tunda matsayinsa yafi
naku dariya suka yi ita kuwa daki ta shiga tayi
wanka ta shirya cikin atamfa super kalar ruwan
kwai ta yiwa fuskarta kwalliya sosai ta kafa
dauri kamar goggoro ta feshe jikinta da
turarruka masu dadi tasa sarka fashion golden
colour ta fito falo lokacin karfe 4 har tayi wuri ta
nema ta zauna tana jiran gawon shanu, ni dai
ummi A'isha ina daga gefe ni ma ina sauraron
zuwan oga lamin.
Ummi A'isha
[3/24, 12:34 PM] Ummi A'isha🏻: [3/24, 10:37
AM] Ummi A'isha🏻: MACE GUDA DAYA TILO..

Na
UMMI A'ISHA
ƒ£1⃣

Tana nan zaune har 5 tayi tuni su hasna sun
tafi sashen mummy ita kuwa junada ta cika tayi
dam kiris ya rage ta fashe, sai 5:30 ya shigo
gidan tana zaune a falo ya bude ya shigo
hankalinsa kwance fuskarsa wasai ganin haka
yasa junada taji ta dada tsarguwa da shi kallo
bishi da shi babu alamun damuwa ko kadan a
fuskarsa sallamarsa ce ta katse ta, ta amsa
fuska babu annuri can nesa da ita yaje ya zauna
tuni ta gasgata zarginta fuskarsa dauke da
murmushin keta yace ina su hasna? Kamar ba
zatayi magana ba tace suna side din mummy
kallonta yayi kwalliyar tata tayi masifar yi masa
kyau gamida jan hankalinsa amma bai nuna
mata hakan ba shi kansa ya san junada first
class ce asahun kyawawan mata kamar yadda
yake first class a sahun kyawawan maza
dagowa yayi yaga ta kafe shi da ido ko kiftawa
batayi wai lfy kuwa? Ya tambayeta lafiyar ce ta
kawo haka tafada tana mai ci gaba da kallonsa
har sai da ta tabbatar da zarginta domin lips
dinsa taga alamun jan baki ajiki a fusace ta
mike yabita da kallo ya ce gobe ki shirya za
muje bauchi banza tayi masa ta shige dakinta
shi kuwa tashi yayi ya hau kan dining yafara
kwasar girkin da ta tanadar masa. Ita kuwa
junada tamkar zata mutu dan kunar rai,
hankalinta duk yabi ya gama tashi ita kam ya
zata yiwa lamin ya daina neman matan nan?
Wata zuciyar tace duk laifinki ne meyasa
alokacin da yazo miki da bukatarsa baki bashi
hadin kai ba? Ai da kin amince dashi kin bashi
kulawa to da babu macen da zata sha gabanki
awurinsa saboda duk matan da zai yi mu'amula
dasu awaje babu wacce zata nuna miki kyawun
halitta, hakika nayi babban kuskure da ban
amincewa lamin ba lokacin da ya bukaceni ta
fadi hakan acikin zuciyarta mikewa tayi tace ya
zama dole na tsaya na gyara kuskure na tunda
wuri.
MACE GUDA DAYA TILO
Na
UMMI A'ISHA
ƒ£2⃣

Falon ta koma akan dining ta ganoshi yana
cin abinci yana waya amma bata hango
fuskarsa saboda ya bata baya hakane ya bata
damar bude idonta sosai tafara kare masa kallo
komai nashi mai kyaune ya hadu ta kowanne
fanni tamkar shi yayi kansa tana nan zaune har
ya gama cin abincin ya tashi ya shiga dakinsa
Jim kadan sai gashi ya fito daga shi sai gajeren
wando kallo 1 tayi masa ta sunkuyar da kanta
kizo ki zuba min ruwan wanka tun kafin ya
karasa ta mike a zuciyarta tana cewa ai dole
kayi wanka dan kai kadai kasan me ka aikata
bathroom din ta shiga ta hada masa ruwan
sannan ta fito ba tareda ta kalleshi ba tace na
zuba maka yawwa thank you taji yafada cikin
tausasshiyar muryarsa fitowa tayi daga cikin
dakin ta nufi nata ta fara shirya kayanta acikin
babbar trolley sai dai acan kasan zuciyarta
kuma tunanin tafiyar nan da zatayi take anya
kuwa idan ta tafi bazai samu damar holewarsa
yanda ya gadama ba? Mts tsaki taja tace nasan
dai duk tsiyarsa bazai kawo mata gidan nan ba
tunda su mummy suna nan sai dai yaje hotel da
wadannan tunane tunanen tagama hada duk
abinda tasan zata bukata. Washe gari da
wurwuri ta tashi ta hada breakfast ta gyara
gidan ta shiga tayi wanka ta fito taci kwalliya
cikin wani leshi orange tasha kwalliya tayi kyau
sosai ta fito kamshi ne kawai ke tashi daga
jikinta tana fitowa ta hangoshi shima har ya
shirya yafito yana zaune yana cin soyayyen
dankalin da ta soya masa yayi kyau sosai cikin
wani lallausan bakin yadi mai tsadar gaske yasa
hula itama baka agogon hannunsa na azurfa ne
sai kyalli da walwali yake kamar kullum kamshin
turaren Phoenix ne ke tashi daga jikinsa kallonsa
tayi acikin zuciyarta tace Kai dai ko wanne kaya
kasa sai yayi maka kyau gaka da son kamshi
kamar me, afili kuwa dan russunawa tayi tace
ina kwana? Kin tashi lfy? Lfy lau kujera itama
taja ta zauna ta hada tea tasha agurguje ta
shiga side din mummy tayi mata sallama tafito
lokacin suma su hasna sun tashi kayanta ta
dauko tafito sukayi sallama ta nufi inda yake
tsaye yana jiranta.
MACE GUDA DAYA TILO...
Na
UMMI A'ISHA
ƒ£3⃣

Wata sabuwar mota katuwa baka taga ya
dauko yazo gabanta ya tsaya su husna ne suka
bude mata motar ta shiga yaja suka fita daga
gidan tana ta dagawa su hasna hannu, kira'ar
sudais ya kunna cikin suratul Yusuf ya kure A. C
din cikin motar lumshe idanuwanta tayi tana
sauraron karatun tana bi acikin zuciyarta kamar
a mafarki taji shima lamin yana bi ahankali
mamaki ne ya cikata ashe dai shima
mahaddacine sai tsabar shagala Allah ya kyauta
tafada cikin ranta gudu yake sosai tun tana
tsorata har ta daina dan ta fahimci yanayin
tukinsa ne haka kafin kace me bacci yayi awon
gaba da ita kallon fuskarta yayi yaga tana bacci
wani kayataccen murmushi ya saki junada
kenan junada zanyi mutukar baki mamaki
yafada acikin zuciyarsa. Karfe 12 suka isa garin
bauchi sai da suka shiga cikin gidan sannan ya
tasheta cikeda mamaki tace har munzo? Eh ga
zahiri kuwa kin gani fitowa sukayi daga cikin
motar suka tasamma cikin gidan suna shiga falo
ta hango ummanta ai da gudu taje ta fada
kanta ta rungumeta shi dai lamin abinma dariya
ya bashi sai yau ya yarda junada muguwar
yarinya ce, dakyar ta daga umman tata suka
gaisa da lamin nan da nan aka cikasu da kayan
ciye ciye waya ummanta tayiwa abbansu tafada
masa zuwansu, office din ya baro yazo suka
gaisa da lamin, sai da lamin yayi sallar azahar
sannan yayi musu sallama ya fito biyo shi
junada tayi tace sai yaushe zan dawo sai kin
ganni nadawo 2 weeks zakiyi, tace to Allah ya
kaika lfy amma dan Allah ka rage gudu, har
cikin ransa yaji dadin maganarta murmushi yayi
mata yace insha Allah yashiga motar ya tafi.
[3/24, 10:40 AM] Ummi A'isha🏻: MACE GUDA

DAYA TILO
Na
UMMI A'ISHA
ƒ£4⃣

Tsayawa tayi har sai da taga fitarsa sannan
ta shiga gida ta na mai addu'ar Allah ya kaishi
gida lfy. Wuni sukayi suna hira ita da ummanta
har Abbanta ya dawo daga office shima suka ci
gaba dashi,sai bayan sallar isha sannan ta shiga
dakinta wanda har yanzu yana nan a kintse
babu abinda aka canja sai kace tana gidan.
Wanka taje tayi tazo ta shirya cikin rigar
baccinta ta haye gado, lamin ne ya fado mata
Allah sarki ko yanzu me yake yi? Ko har yayi
bacci? Ko kuma kallo yake? Wayarta ta jawo ta
fara kiran husna ringing 3 ta daga tana fadin
Allah yabar Antynmu dariya junada tayi sannan
tace yagida? Gida lfy ya kika tarar da mutan
gida? Duk lfy ina hasna? Hasna tana falo ni
kuma na shigo daki, ok ina yayanku? Gashi can
na hangoshi ta window yana fitowa daga side
din daddy, wanne irin kaya ne ajikinsa? Body
hug baka da boxer baki ajiyar zuciya junada
tayi sannan tace kije kice ina gaidashi da fatan
ya isa gida lfy to Anty angama, mikewa husna
tayi ta fita zuwa inda ta hangoshi yana zaune
acikin wata yar karamar runfa wadda aka
tanada domin hutawa da wasu yan kujeru aciki
sai kace a turai sannu yaya yawwa sannu dama
Anty junada ce tace ince tana gaisheka da fatan
ka dawo gida lfy? Murmushi yayi sannan yace
kice ina amsawa sannan kuma na dawo lfy da
fatan zatayi bacci lfy to tafada ta juya tana cikin
tafiya junada ta kirata ta daga tafada mata
sakon murmushi junada tayi tace nagode kigaida
su mummy ta kashe wayar ko ba komai
hankalinta ya dan kwanta tunda taji halin da
yake ciki amma kuma sai ta tsinci kanta da son
ganinsa a wannan lokaci fatanta daya Allah yasa
ba da wata manufa ya dawo da ita gida ba.
MACE GUDA DAYA TILO...
Na
UMMI A'ISHA
ƒ£5⃣

Juyi kawai takeyi amma bacci ya kauracewa
idonta tunanin mijinta ne kawai ke addabarta da
kyar ta samu bacci ya dauketa. Da safe da
misalin karfe 10 ta kira husna ta tambayeta ina
lamin? Murmushi husna tayi tace yana side
dinku yana bacci inajin bai tashi ba cikeda
damuwa junada tace dan Allah kije ki gano min
shi tashi husna tayi ta fita tana ta faman mita ni
kam ai na shiga uku kuma da haka takarasa
sashen nasu ta lalleka dakunansa amma baya
ciki dakin junada ta buda abin mamaki hangoshi
tayi baje akan gadon junadan yanata sharar
bacci rufe kofar tayi tajuya ta fita tafara kiran
junada tana dagawa ta fara bata labarin lamin
wani dadi junada taji ashe dai yafara damuwa
da ita yanzu. Abin har ya zamewa husna jiki
domin kullum junada sai ta kirata ta tambayi
lamin hatta kalar kayan da yasa sai an fada
mata kuma sai taji shin ya fita ko bai fita ba da
haka har tayi sati 1 da zuwa aranar kuma ta tafi
azare gidan kanwar mamanta mami da niyyar yi
mata kwana 2 nan da nan mami ta fara yi mata
dure dure da tsume tsume ita junada abin ma
har isarta yayi aranta kuwa fadi take ai wanda
aka yimin a sudan ma har yanzu yana nan
ajikina kwananta 2 ta dawo gida cikeda kayan
gyare gyaren da mami ta hado mata. Ranar da
ta dawo aranar yayunta suka dawo daga
makaranta Khalid da Amir harda cousin dinsu
Mahmud wanda shima duk tare suke karatun a
waje kar kaso kaga murna wurin junada haka
tashiga cikinsu suka baje ana ta hirar yaushe
gamo kasancewar ko lokacin bikinta basu samu
sun dawo gida ba.
Ummi A'isha
[3/24, 12:34 PM] Ummi A'isha: [3/24, 10:45 AM]
Ummi A'isha🏻: MACE GUDA DAYA TILO

Na
UMMI A'ISHA
ƒ£6⃣

Yanzu tafi jin dadin zaman gidan saboda
dawowar su Khalid kullum wuni suke suna hira
amma fa tunanin lamin yana nan makale acikin
zuciyarta, waya kuwa kullum sai ta kira husna
taji labarin lamin amma hankalin ta yadan
kwanta domin kullum yana gida baya fita koda
wanne lokaci idan ta tambayi husna ya fita sai
tace a'a yana wurin daddy ko kuma yana side
din su. Ahaka har hutun nata ya kare husna ce
takirata take ce mata Anty yaya yace ki shirya
ranar Saturday zai zo ku tafi domin ranar
Monday zamu koma sch murmushi tayi to husna
kice masa zan shirya, nan da nan tafara harhada
kayanta wuri guda. Hakan kuwa akayi ranar
Saturday sai gashi wurin karfe 12:30 lokacin da
ya shigo falon yayyun junada suna zaune hannu
ya basu suka gaggaisa har umma tafito itama
ya gaida ta dakin junadan ta leka ta ganta tana
shiryawa tace to kifito yazo idan kukayi sallah
kuka ci abinci sai ku tafi to umma ina zuwa inji
junada tana gama shiryawa ta fito ta sameshi
zaune a falo yasha waganbari milk colour da
hula milk colour ya gyara sajensa fuskarsa tayi
kyau hannunsa ya daura agogon fata milk
colour gabansa ta karasa tana fadin yaya lamin
sannu da zuwa amsawa yayi yana kallonta tayi
kyau sosai cikin bakin material din data sa
kallon da ya lura Mahmud yana yima ta ne
yasashi fadin kije ki dauko mayafinki to tafada
ta tashi tafita. Saida suka ci abinci sukayi
sallah sannan suka fito da niyyar tafiya Khalid
ne yayi dariya yace autar umma kin manta
wayarki awurin mahmud kallon khalid din tayi
tace wlh naso na manta kuwa hangowa
mahmud din tayi shida amir suna tahowa tace
yawwa gashi nan ma shida yaya amir shidai
lamin yana tsaye baice komai ba har suka
karaso wurinsu khalid ne yace mahmud ka bawa
auta wayarta zasu tafi dariya Mahmud din yayi
yace ai ba ita ta baniba warta nayi dan haka
nima ba bata zanyi ba tunda lokacin danace ta
aramin guduwa tayi.
MACE GUDA DAYA TILO...
Na
UMMI A'ISHA
ƒ£7⃣

Guduwa tayi wurin mummy dan haka nima
bazan bata ba kallon khalid tayi tace yaya
Khalid dan Allah karbo min wayata, karbo mata
yayi ya mika mata shi kuma mahmud yaci gaba
da fadin ai wlh yarinya ba don kin gudu ba da
sai na murde hannunki na kwace, kallonsa lamin
yayi cikin kunar rai tuni zuciyarsa tafara tafasa
motar ya bude yashiga itama shiga tayi ta
zauna hannu suka fara daga musu amma lamin
ko kallonsu bai yi ba saboda ransa ya gama
baci ai nan take ya murtuke fuska idanuwansa
suka rine sukayi ja acikin ransa fadi yake warta?
Ya warci waya a hannunta? Yabita ta gudu
wurin umma? Lallai ashe ma wasa sukayi tunda
harda su guje guje yayi kyau yafada afili ita dai
junada tuni ta gama tsurewa saboda bata san
meya bata masa rai ba ko kadan ba ta zata
maganganun mahmud sunada nasaba da bacin
ransa ba shiyasa taja bakinta tayi gum ahaka
har suka isa garin yola. Yamma lis suka shiga
gidan amma har yanzu lamin akule yake da ita
yana parking ko kallonta baiyi ba yafice ya shige
side dinsu ita dai batasan me tayi masa ba,
fitowa itama tayi ta kwashi kayanta ta shigar
cikin falonta sannan tashiga wanka tayi salla ta
nufi side din mummy tana shiga su husna suka
taso suka rungumeta cike da zolaya husna tace
yau nima zan huta da tambaye tambayen da ake
min hasna tayi caraf ta cafe ai dan an san zaki
iyane shiyasa aka saki ni da aka san bazan
iyaba ai kinga ba asaka ni dariya suka saka
mummy tace kun karata dai masu surutun tsiya
karasawa junada tayi ta durkusa ta gaidata
sannan ta tashi takoma side dinta yan rakiyarta
suna biye da ita abaya.
MACE GUDA DAYA TILO...
Na
UMMI A'ISHA
ƒ£8⃣

Suna shiga ta fada kitchen ta dafa musu
indomie da kifi ka kawo musu shi kuma lamin ta
dora masa tasa akan dining, shiru shiru har dare
yayi bai fito ba yana can acikin dakinsa ita
kuma tsoron yi masa magana take, har suka
gama hirarsu suka shiga daki bai fito ba, abin
yayi mutukar damun junada domin bata son
bacin ransa ita ba abun taje ta tambayeshi ba
wata zuciyar tace mata ki bari sai ya huce
tukunna sai ki tambayeshi inyaso alokacin sai ki
bashi hakuri gaba kuma sai ki kiyaye da wannan
shawarar tayi amanna. Washe gari ta tashi ta
gyaggyara gidanta tayi komai amma girkin data
ajiyewa lamin yana nan yadda yake bai ko buda
ba ranta taji ya sosu to shi wannan me nayi
masa ne? Ta tambayi kanta amma ganin bata
da amsa yasa ta ci gaba da abinda take. Wasa
wasa har tayi sati daya da dawowa lamin baici
abincinta ba asalima ita tun daga ranar da suka
dawo daga bauchi bata kara saka shi a idanunta
ba kuma yana gidan, da haka suka koma
makaranta kullum tana busy bata da lokacin
kanta gashi tunanin halin da lamin yake ya
gallabi ruhinta ahaka har sati 3 da dawowarta
amma lamin ya daina cin abincinta ya daina
kiranta ta hada masa ruwan wanka tama daina
ganinsa kwata kwata dan haka sai ta tattara
zamanta ta mayar side din mummy ita dasu
hasna bacci ne kawai yake dawo dasu side din
junada. Yau lecture tayi mata zafi ga test din
unexpected da wani malami yayi musu ga
lecture note da aka bayar akace kowa ya siya
ga ta gaji dan haka sai kawai ta kira wani dan
department din su wanda ta fahimci yanada
hankali ta bashi sakon.
[3/24, 10:49 AM] Ummi A'isha🏻: MACE GUDA

DAYA TILO...
Na
UMMI A'ISHA
ƒ£9⃣

Tabashi sakon tace dan Allah ya siya mata
lecture note din ya kawo mata gida cikin
girmamawa yace hajiya inane gidan naki, kasan
gidan SSG? Eh tsohon gidansa nasani amma
ban san sabon gidan da ya koma ba, bakasan
new government house ba? Cikin sauri yace
nasani hajiya, to kana zuwa government house
daga gefen dama ba gefen hagu ba, gefen hagu
gidan deputy governor ne nagefen dama shine
namu, wani dan kati ta ciro ta mika masa
( visitors card) tace ungo wannan sai ka
nunawa securities din gidan zasu barka ka shiga
dan Allah ka kawo min ayau dan karatu nake
son zanyi to hajiya zanzo insha Allahu ya juya
yatafi yana ta faman murna domin ko ba komai
yau zaije gidan SSG wanda ba kowane yake
shiga ba sai mai kwalli a ido irinsu hawwa jabo
da Adda Benaxir, ita kuwa junada juyawa tayi ta
nufi motarta domin yunwa takeji sosai ga tagaji
su husna kuwa tuni sun dade agida dan tun
12'suka gama lectures dinsu ganin bata gama
ba yasa sukayi waya gida aka turo musu driver
ya daukesu. Tana zuwa gida side din mummy ta
wuce anan taci abinci tayi salla sannan ta wuce
sashen ta,takwanta tayi bacci sai wurin 4 ta
tashi tayi wanka taci kwalliya tayi sallar la'asar
ta fito ta tafi wurinsu hasna tana fitowa ta
hango wani daga cikin ma'aikatan gidan da
kayan sojoji yana dosota yana zuwa ya dan
rissina yace hajiya kina da visitor yana ina?
Gashi can awurin second Gate,to ina zuwa ciki
ta koma jim kadan ta fito ta nufi wurin,wannan
dan department din nasu ta gani cikin sakin
fuska tace sannu yawwa sannu hajiya gashi nayi
miki guda biyar bayan kin taho aka bada sauran
murmushi tayi tace amma nagode ta karba ta
mika masa kudi yan dari dari nidai ummi Aisha
ban san ko nawa bane yawan kudin, cikin
girmamawa yace nagode nagode hajiya ah nice
da godiya meye sunanka hajiya sunana lamin
wani kayataccen murmushi tayi sunan maigida
nane to hajiya nagode Allah yasaka da alkhairi
sai anjima ya juya yatafi itama juyowar tayi da
nufin tafiya side din mummy kawai sai hango
lamin tayi yana tsaye yafito daga side din daddy
yana sanye cikin wata body hug coffee colour an
zana hannu ajiki an rubuta show time da wando
jeans blue yayi mutukar kyau yana jingine ajikin
motar daddy ya harde hannuwansa akan kirjinsa
ashe duk wannan abun da yafaru akan idonsa
ne.
MACE GUDA DAYA TILO...
Na
UMMI A'ISHA
ƒ£0⃣

Nufuto yayi fuskarsa a daure kamar bai taba
dariya ba yaja hannun ta bai tsaya ako ina ba
sai falonsu ya mayar da kofa ya kulle ya zare
key din, ya kalleta yana ta faman huci waye
wancan? Cikin tsawa yayi tambayar wadda tayi
mutukar gigita junada badake nake magana ba?
Nace waye wancan wanda yazo wurinki? Cikin
dakewa tace dan ajinmu ne ya kawo min lecture
notes, wato ke bakida hankali ko? Kula maza
kikeyi baki san hakkin dake kanki ba ko? Bude
idonta tayi cikin mamaki tafara kallonsa maza?
Tafada acikin zuciyarta to ita wanne namiji ta
kula awaje? Yaci gaba da yayyafin masifa ke na
lura bakida hankali kamar yadda sauran mazan
dake kulaki na fuskanci dakikai ne marassa ilmi,
da aurenki zaki rinka biya wasu shashashu wai
har kuna wasa saboda tsabar jahilci, cikin tashin
hankali ta kalleshi tace wa na kula har mukayi
wasa? Au tambayata ma kike? To wannan
dakikin dan uwan naki mahmud da yake shi
jahiline mai kwakwalwar kifi shine zai rinka
kokawa dake alhalin da aurenki to wlh wannan
yazama na karshe duk ranar da yasake kulaki
sai na daure dan iska, sai yanzu junada ta gano
ma'anar fushin da ya ketayi da ita to amma
wannan ai fadan rashin gaskiya ne, muryarsa ce
ta dawo da ita gareshi inma banda tsabar rashin
tunani tayaya mutum zai tsaya yayi wasa da
matar da ba tasa ba sai irinsu tsinannu
gogaggun yan bariki nan da nan junada ranta
yafara baci da zagin da yake yiwa dan uwanta ai
wannan cin fuska ne kuma ayanda ta fuskanta
zuwan wannan dan ajin nasu bai bata masa rai
sosai ba kamar yadda maganar Mahmud ta bata
masa rai, kallonsa tafara yi cike da takaici tace
dan Allah dakata min kar ka kara zagar min dan
uwa saboda kai xan iya canzaka amma shi
bazan taba iya canzashi ba domin ahalinmu ne,
kanata wani ikirarin ina kula maza ba gara ni ba
kaifa? Tsawa ya daka mata wadda saida taji yan
hanjin cikinta sun juya oh! Kin fara son maza
ko? Nace kin fara son maza? Lallai ba laifin ki
bane laifinane cikin bakin ciki tace eh nafara son
mazan kai mata nawa ka kawo cikin gidan nan
kayi fasikanci dasu? Ai ko falon nan da ace
yanada baki ya isa bada shaida, ni kuwa duk
kule kulen mazana ban taba kawowa gardi cikin
gidan nan ba kallonta yafara yi sama da kasa
haka kikace? Nace haka kikace? To yau za ayita
ta kare akan wanccan shashan dan uwan naki
kike gayamin bakar magana? Tabbas kin fara
son maza dan haka yazame min dole ayanzu na
dauki mataki.
Ummi A'isha
[3/24, 12:34 PM] Ummi A'isha🏻: [3/24, 11:00
AM] Ummi A'isha🏻: MACE GUDA DAYA TILO...

Na
UMMI A'ISHA
ƒ£1⃣

Yana fadin haka ya danko gashin kanta ya
nufi cikin dakinta da ita suna shiga ya cillata
kan gado ya rufe kofar ya zare key din ya jiyo
yana ta huci ita kuwa junada duk da haka
bakinta bai mutu ba fadi take wlh sai dai idan
kasheni zakayi ka kasheni amma babu wanda ya
isa ya rabani da dan uwana domin jinina ne
murmushin takaici yayi yace ai kuwa yanzu
zakiga jinin naki yarinya belt din jikinsa taga ya
cire da sauri ta runtse idonta don duk zatonta
dukanta zaiyi tana nan sankame taji shi ya zo
kusa da ita ya jefa gado cikin sauri ta bude
idonta ganinshi tayi dagashi sai gajeren wando
ai tuni suka fara kokawa ganin bata da nasara
yasa tafara kurma ihu amma sai dai kash! Babu
wanda zai jiyota, hakuri tafara bashi dan Allah
yaya lamin kayi hakuri wlh bazan kara magana
da kowanne namiji ba murmushin mugunta yayi
yace wlh yau idan kinga na kyaleki to
numfashina ne ya yanke amma indai ina
numfashi to sai na rabaki da abinda kike
tunkaho dashi daga yau zaki daina kula wani da
namiji a doron kasa, hannuwanta yahada duka
ta baya ya rike kafin kace kwabo muryar ta har
ta disashe tun tana iya ihu har ta dawo bata
iyawa banda hawaye babu abinda ke zuba a
idonta, shi kuwa lamin baima san a duniyar da
yakeba ba saboda gaba daya junada ta gama
rikitashi duk da dama yana yakinin zai sameta
haka to amma sai yaga ya sameta fiye da
tunaninsa. Sai bayan sallar isha'i sannan ya iya
kyaleta lokacin ko motsi bata iyawa shi kansa
saida ya tsorata saboda yanayin daya ganta
gaba daya ta jigata marabar ta da matacce
numfashi, sai alokacin yaji tausayinta ya darsu
azuciyarsa shi kansa yasan baiyi mata ta dadin
rai ba saboda lokacin ransa yagama baci
afusace yake alhalin kuma bai kamata yabi da
ita ta haka ba sam bai tausaya mata ba yanda
yasaba bida yan matansa haka yabida ita alhalin
kuma yasan akwai banbanci su da ita, ahankali
ya rungumeta yafara hawaye acikin zuciyar sa
yace Allah nagode maka da kabani kamilalliyar
mace hakika nasan wannan rahama ce babba
kayi min batare da ka duba halayyata ba, duk
yadda na kasance ina saba maka amma sai ka
dauko kamilalliyar mace kabani,baka bani
mazinaciya Irina ba ya Allah nayi maka alkawari
daga yau bazan kara aikata zina ba har nadawo
gareka, zan tsaya a iya gonata daka albarkaceni
da ita.
MACE GUDA DAYA TILO....
Na
UMMI A'ISHA
ƒ£2⃣

Hawaye ne yaci gaba da gudana akan
kumatunsa na tausayin matarsa, shi kansa
yasan ta wahala dayawa awa 4 ana abu 1
ummm tom ummi A'isha dai bata da ta cewa,
ganin bacci ya dauketa yasa yatashi yashiga
toilet dinta yayi wanka ya fito haka kawai ya
samu kansa cikin wani nishadi ai rayuwar aure
tayi yafada acikin ransa domin tunda yake
yawon bin mata bai taba tsintar kansa acikin
yanayin da ya samu kansa yau ba, dakinsa yaje
ya saka jallabiya yayi sallar magrib da isha
sannan yafito afalo ya tsinkayo wayoyinsa yana
dubawa yaga miss called din daddy wurin 5
murmushi yayi yasan dan bai ganshi a masallaci
bane shiyasa yakira yaji dalili to amma idan ya
tambayeshi me zaice? Ai gaskiya da kunya dan
haka sai kawai ya tura masa txt da cewa kanshi
ne yake ciwo kuma shine da yasha magani
bacci ya dauke shi sai yanzu ya tashi, dakin
junada ya nufa lokacin ta farka tana tuno abinda
ya faru tsakaninta da lamin dazu bude kofar ta
ga anyi shine ya shigo daga shi sai gajeren
wando runtse idonta tayi tafara fadin dan Allah
yaya lamin kayi hakuri ka kyaleni wlh zan mutu
ahankali yazo gefen gadon ya zauna yakamo
hannunta ya rike cikin nashi yafara kama yan
yatsunta daya bayan daya yana murzawa,
junada! Taji ya ambaci sunanta saura kiris ta
sume domin ji tayi duk duniya babu wanda ya
iya fadar sunanta kamar shi, yaci gaba da cewa
ki yafe min abinda nayi miki nasan na wahalar
dake ban biki asannu ba amma dan Allah kiyi
hakuri kinji hawaye taga yafara bin kumatunsa
ahankali ta girgiza kanta alamun ya daina kuka
hannunta ya saki ya tashi yashiga toilet ya
hada mata ruwan wanka yadawo dakin yace
tashi kije kiyi wanka, bazan iya tashi ba caraf ya
dauketa ya kaita toilet din wanka yayi mata ya
gyarata tsaf sannan yadawo da ita dakin ya
saka mata doguwar riga sannan ya shimfida
mata sallaya daga zaune tayi sallolin shi kuma
ya cire bedsheet din ya shimfida mata wani tana
idarwa ya cire mata doguwar rigar ya saka mata
rigar bacci ya dauketa ya dora akan gado yazo
kusa da ita ya zauna me zan dafa miki nasan
kina jin yunwa ahankali tace tea kawai zansha
ka duba kitchen akwai ruwan zafi acikin flask da
sauri ya mike ya Shiga kitchen din ya hado
mata tea mai kaurin gaske kamar koko ya kawo
mata dakyar ta tashi zaune ya fara bata har ta
shanye sannan ya kwantar da ita ya fita kafin
yadawo har bacci yayi awon gaba da ita.
MACE GUDA DAYA TILO..
Na
UMMI A'ISHA
ƒ£3⃣

Yana shigowa yaga har bacci ya dauketa
dan haka kusa da ita ya je yakwanta yashiga
cikin jikinta, can cikin dare yaji zazzabi ya rufeta
jikinta yayi zafi zau kamar wuta cikeda
tausayawa yaja bargo ya rufesu sai dai shi baiyi
wani baccin kirki ba motsi kadan zai tashi ya
haskata yaga halin da take sannan zai kwanta
ana jimawa zai kara tashi da haka har gari ya
waye shi tun asuba yayi salla amma bai tasheta
ba gudun kar ya katse mata baccinta sai wurin
6 sannan ta tashi yana kwance agefenta ta dan
kalleshi sai taga idanuwansa arufe duk azatonta
bacci yake dakyar ta iya tashi kamar mai koyon
tafiya tafara takawa ahankali ya bude idonsa ya
bita da kallo cikeda tausayawa ahaka yaga ta
fito ta shimfida sallaya tasa dogon hijabinta har
kasa zama tayi saboda ba zata iya tsaiwar ba
kwalla ce yaji ta ciko masa ido yayi saurin
gogewa ahaka ta idar da sallar ta dawo gadon
ta kwanta, kanta ya dago ya kwantar akan
kirjinsa yace sannu junada yaya kike jin jikin
naki, zazzabi nakeji yana neman rufeni kuma
kaina sai ciwo yake sannan jijiyoyin jikina jinsu
nake kamar ana tsintsinka min su, cinyoyina
kuma kamar ana sassara min gashi sunyi tsami
kuma sunyi min nauyi,cikin tausayawa yace
sannu bari naje na nemo miki magani, yana
fitowa falo yaji ana kwankwasa kofar budewa
yaje yayi husna da hasna yagani a tsaye yaya
ina kwana lfy ya akayi? Gurin Anty mukazo, me
zakuyi mata? Mun jita shiru tun jiyane shiyasa,
lafiyar ta lau,Ku koma ku shirya mana breakfast
zan zo na karba yana gama fadin haka ya
maida kofar ya rufe yashiga dakinsa ya saka
jallabiya da dogon wando yafito saida yasa key
ya kulle kofar falon sannan yafita motarsa ya
dauka ya tafi wani chemist ya siyo mata
magunguna sannan ya dawo gidan, side din
mummy ya shiga ya dauko kayan breakfast din
yashiga side dinsu lokacin har ta tashi daga
bacci tayi wanka da ruwan dumi ta gaggasa
jikinta babu laifi ta danji dama dama tayi
kwalliyar ta cikin wani brown din leshi tana
zaune a falo ta kunna kallo, yana shigowa ta
sukwi da kanta kasa bata yarda sun hada ido ba
gabanta yazo ya ajiye abincin ya zuzzuba mata
soyayyiyar doya da kwai da farfesun hanta,
sauko da ita yayi ya dorata akan cinyarsa yafara
bata abaki gaba daya idonta sunyi jawur
fuskarta ta kumbura abinka da farar mace sai
kace sweet choco kawata, ahaka har ta koshi ya
bata maganin tasha sannan shima ya dan ci
abincin ya tashi ya shiga dakinta ya gyara mata
ya share ya kunna turaren wuta yadawo falonma
ya gyara ya shiga kitchen ya wanke mata
kwanuka ya share sannan ya dawo falon da
take,kallo kawai take binsa dashi daga shi sai
best da gajeren wando.
[3/24, 11:04 AM] Ummi A'isha🏻: MACE GUDA

DAYA TILO...
Na
UMMI A'ISHA
ƒ£4⃣

Falon yadawo ya feffesa air freshener yasaka
turaren wuta bugun kofar da yaji ana yine
yasashi tashi ya leka su hasna ne cikin shirin
tafiya makaranta lekowa yayi yace ya akay?
Yaya dama mun shirya ne shine muka biyowa
Anty, kuyi tafiyarku ita yau bazata ba sai kun
dawo kofar ya mayar ya rufe, wunin ranar dai
bai huta ba dukkan ayyukan gidan shine yayi
mata har tausayi yabata saboda yanda yaketa
nan nan da ita gashi yanada lecture amma duk
ya share yaki zuwa shi ta lafiyar matarsa yake.
Haka ya rinka bata kulawa har na tsawon sati
daya lokacin da ya fuskanci ta warware ne
yafara fita kuma aranar ya kawo mata yan aiki
guda 3 yace bai yadda tayi kowanne aiki ba in
banda girki da gyaran dakinsa,wata soyayya mai
wuyar fadi suke nunawa junansu, su husna kuwa
tuni sun koma sashen mummy domin abin yafi
karfinsu agabansu lamin yake kissing din junada
ko ya rungumeta,yauma suna zaune acikin falo
dukansu suna kallo ya dawo daga office ko
kunyar su baiji ba yaje yashige cikin jikin junada
ahankali ya lalubi bakinta yasaka cikin nashi
hasna ce tace kinga husna zo mu tafi duk
lokacin da suke da bukatarmu sa kiramu hakan
kuwa akayi suka tashi suka tafi wurin mummy,
ita kuwa junada dama tama manta da suna
wurin domin ta dade tana kaunar jajayen lips din
lamin dan suna mutukar burgeta. Ahaka
rayuwarsu tayi ta tafiya cikin farin ciki
alokacinne Kausar suka dawo daga kasar
Uganda ita da Abdulrahman cikinta ya tsufa
sosai, lokacin itama junada ta soma nata yan
jinyace jinyacen da zazzabi ganin abin yayi yawa
yasa lamin yakira mata likita har gida yana
dubata ya ta tabbatar musu tana dauke da juna
biyu na wata 2 tuni lamin yafara murna wai
shine zai haifi dan kanshi, murmushi ya saki mai
kayatarwa junada tace lfy? Kallonta yayi yace
abin ne ya burgeni dalibata zata haifa min yara,
murmushin itama tayi tace ai malamin ne akwai
iya daukar fansa dariya yayi yajawota jikinsa ya
rungumeta yace duk cikin friends dina fa ni kadai
ne nayi auri gashi har zan haihu dariya itama
tayi tace to ai kayi dabara nasan nice zan rigaka
tsufa tunda kai namiji ne murmushi yayi ya
kama hannunta yayi kissing dinsa sannan yace
no ni yanzu inada 27 ke kinada 21 tare zamu
tsufa, malami dai ya auri dalibarsa.
MACE GUDA DAYA TILO....
Na
UMMI A'ISHA
ƒ£5⃣

Ahaka ya shagaltar da ita da soyayyarsa mai
wuyar fahimta. Washe gari kausar ta haifi
yaronta santalele mai kamada lamin sak dan
haka ranar suna ma sunan lamin din yayansa
yasakawa yaron, yanzu rayuwa tayiwa junada
dadi domin ta fahimci ita kadai ce MACE GUDA
DAYA TILO acikin zuciyar mijinta yana bata
dukkan kulawa kuma ahaka yayita tayata renon
cikinta har ya isa haihuwa ranar da zata haihu
lamin baya nan dan haka sai dawowa kawai
yayi yaga ta haifi jariranta masu kama dashi
sak, su husna kuwa tamkar zasu cinye su don
so shi kanshi lamin yaran sun shiga ranshi
dayawa haka akasha shagalin suna inda yaran
sukaci sunan mahaifinsa da mahaifin junada ana
kiransu sudais da shurem ansha buduri sosai
washe garin suna mami kanwar umman junada
ta tafi da ita bauchi tace sai bayan sunyi arba'in
zasu dawo lamin kuwa bai so ba dan babu
yadda zaiyi ne amma baiso sukayi nesa dashi
ba, ita kuwa Mami tayi hakane domin ta samu
damar gyara masa ita, duk karshen sati yake
zuwa bauchi wurinsu da haka har suka cika
arba'in saida suka dan zazzaga dangi sannan
suka dawo yola lamin ne yaje dakansa ya
daukosu yaci gayu cikin wani farin boyel mai
shegen kyau da tsada idan kaganshi bazaka
taba cewa yana da mata ba balle har kace ya
ajiye yara biyu.
[3/24, 11:08 AM] Ummi A'isha🏻: MACE GUDA

DAYA TILO.....
Na
UMMI A'ISHA
ƒ£6⃣

Haka ya debo su yana cike da doki domin shi
kansa yasan yayi missing din junada, la'asar lis
suka karaso gida cike da tsarabar bauchi su
husna sai murna akeyi shi kuwa lamin alla alla
yake su kebe shida matarsa domin ya tabbatar
mata da cewa yayi rashinta. Ahaka suka ci gaba
da rainon yaransu kuma alokacinne aka sanya
ranar bikinsu husna zasu auri wasu twins yayan
Governor din garin zamfara, dan haka suna
gama karatunsu aka fara bikin junada itace uwar
biki domin itace akan komai yan biyunta kuwa
har sunyi wayo sun girma ba adade da bikinsu
hasna ba ta yayesu lokacin sun cika 1 year.
Haka suka ci gaba da rayuwarsu cikin farantawa
juna tareda kyautatawa junansu ayanzu auren
ramuwar gayya yazama auren soyayya. Yau an
tashi da sanyi junada ta shirya cikin wani jeans
da riga body hug ta dora katuwar riga sanyi
asama ta nufi dakin lamin yana kwance yana
bacci shida yaransu murmushi tayi ta juya
tafice. Da yamma yafito cikin wata riga t. Shirt
green da bakin wando ya isketa afalo tayi kyau
tamkar wata budurwa ta bayanta yaje ya
rungemata tattausan hannunta tasa ta shafo
sumar kansa tace naga kayi kwalliya sai ina?
Neman aure ai tuni tafara kwalla aure ? Dariya
yayi yace dauko gyalenki ki rakani da gudunta ta
dauko ta fita ta sameshi a mota shida yan biyu
suna jiranta cikin garin yola suka shiga basu
zame ko ina ba sai state university yola suna
zuwa yafito yashiga cikin hall din inda dalibai
sukayi dafifi suna jiransa, test ya rubuta musu
yana cikin rubutunne yan biyu suka shigo cikin
hall din dagudu sudais ne agaba shurem ya
biyoshi cikin muryarsa ta yan yara yace daddy
help me pls dagudu yazo ya rungume lamin
cikin sauri lamin ya dagashi sama yana fadin
wooh! Bai kamaka ba gaba daya yan ajin suka
sa dariya wasu kuwa mamaki suke yanzu
wannan malamin dama yana da aure? Sun
ganshi dan yaro dashi ahaka yagama yi musu
test din suka nufo gida akan hanyarsu ta
dawowa ne yakalle junada yace yanzu idan
akace miki zanyi aure sai ki yarda? Kallonsa
tayi tace ehh mana murmushi yayi yace to ni
babu auren da nake nema domin ke kadai kin
isheni kuma ke kadaice MACE GUDA DAYA TILO
acikin zuciyata, kwantar da kanta tayi ajikin
kafadarsa tana cewa na gode mijina.
Alhamdulillah!
Anan nakawo karshen labarin MACE GUDA DAYA
TILO, barayin fasaha kuji tsoron Allah ku daina
yimana editing din littattafanmu batare da
izininmu ba, duk wanda ya canza min wannan
labarin ko ya cire sunana yasa nasa, ko yacire
number na,ko yayi min editing Allah ya isa ban
yafe ba.
Fatan Alkhairi gareki
Halamcy
Jinjina ga yan uwana marubuta
Fatima zarah ( d writer of xarah)
Kausar m Hassan ( d writer of tsaka mai wuya)
Serdeyeer ( d writer of miss Aysha)
Zainab Rogo ( d writer of auren gida)
Hafsat bounzer ( d writer of rabuwa da masoyi)
Aysha chuchu ( d writer of Duniyarmu)
Dorlin choco ( d writerof Aysha Noor)
Benaxir oumar ( d writer of kalma daya)
Hawwa jabo ( d writer of wacece ita)
Maman Khadija ( d writer of ni marainiya ce)
Maman Nana ( d writer of Mairo)
Cyama galadima ( d writer of Rayuwar rufaida)
Bebeelo ( d writer of kaddararmu)
Humaira ( d writer of samra)
Uhm! Yau fa abin na marubuta ne, yan uwa
makaranta kuyi hakuri sai mun hadu a labari
nagaba mai suna..... Nice taku akoda yaushe
sunan nawa bai canza ba UMMI AISHA

@BABA-MONO-HAXOR


No comments:

Post a Comment

Featured post

[Album] Best Of Nura M Inuwa (Manyan Mata)

Kamar yadda kuke gani aiki ya riga ya kawo gaban koshi.  Saboda haka muna taya wannan mawaki ganin ya fitar da wannan wakoki domin farantawa...

Subscribe For Latest Update

Ads Here